kase kashen kana nan rassa

lis din Hadisai

1. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance damantawa tana kayatar da shi, a sanya takalminsa, da taje kansa, da tsarkinsa, kai da sha'aninsa duka.
عربي Turanci urdu
2. Daga ciki akwai fadin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare cikin hadisin ceto:
عربي Turanci urdu
3. Ban taɓa ganin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi yana ƙyaƙyata dariya ba, har inga ƙarshen ganɗarsa ba, kawai ya kasance yana murmushi. - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
4. Kada ku yi salla a kanku. Kada kuyi addu’a akan yayan ku, kar ku kira kudin ku, kar ku yarda da Allah na awa daya da aka gabatarda kudiri kuma zai amsa muku
عربي Turanci urdu
5. "Idan ɗayanku ya ga wani abu a mafarkinsa da yake son sa to shi daga Allah ne, sai ya godewa Allah a kansa kuma ya bada labarin shi, idan kuma ya ga wanin hakan daga abinda yake ƙi, to kawai shi daga Shaiɗan ne, to sai ya nemi tsari daga sharrinsa, kuma kada ya fadawa kowa, to shi (mafarkin) ba zai cutar da shi ba".
عربي Turanci urdu
6. "Wanda ya reni 'yan mata biyu har suka balaga zai zo ranar alƙiyama ni da shi" sai ya dunƙule yatsunsa.
عربي Turanci urdu
7. :
عربي Turanci urdu
8. : :
عربي Turanci urdu
9. Na kasance tare da Sa'eed bin Jubair sai ya ce: Wanene a cikinku ya ga duniyar da ta share jiya? Na ce: Ni ne, sai na ce: Amma ni ba na cikin sallah, amma an yi min duri
عربي Turanci urdu
10. . : :
عربي Turanci urdu
11. Na rasa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a wani dare a shinfiɗa sai na lalube shi sai hannuna ya faɗa akan cikin diga-digansa alhali shi yana cikin masallaci alhali su suna a kafe, alhali shi yana cewa: @"Ya Allah ina neman tsari da yardarKa daga fushinKa, da kuma rangwaminKa daga uƙubarKa, kuma ina neman tsari da Kai daga gareKa ba zan iya ƙididdige yabo gareKa ba kamar yadda Ka yabi kanKa".
عربي Turanci urdu
12. "Shin ba zan baku labarin 'yan aljanna ba? Duk mai rauni da ake rainawa, da zai rantse da Allah zai kuɓutar da shi, shin ba zan baku labarin 'yan wuta ba? duk mai ƙaton ciki mai kaushin rai mai girman kai".
عربي Turanci urdu
13. :
عربي Turanci urdu
14. "Mafarki na gari daga Allah ne, mummunan mafarki kuwa daga Shaiɗan ne, idan ɗayanku ya yi mummunan mafarkin da yake jin tsoronsa to ya yi tofi a hagunsa, kuma ya nemi tsarin Allah daga sharrinsa, to cewa shi ba zai cutar da shi ba".
عربي Turanci urdu
15. : :
عربي Turanci urdu
16. Akwai matakai guda dari a Sama wanda Allah ya tanadar wa mujahidai a tafarkin Allah, tsakanin darajoji biyu kamar tsakanin sama da kasa
عربي Turanci urdu
17. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Allah - Mai girma da ɗaukaka - Yana cewa: @ Ni ina inda zatan bawaNa yake, kuma Ni ina tare da shi lokacin da yake ambatona*, idan ya ambaceNi a cikin ransa zan ambace shi a cikin raiNa, idan ya ambaceni a cikin mutane zan ambace shi a cikin mutanen da suka fisu alheri, idan ya kusantoNi taki (ɗaya), Zan kusanto zuwa gare shi zira'i (ɗaya), idan ya kusanto zuwa gareNi zira'i (ɗaya), zan kusanto gare shi faɗin hannaye, idan ya zo miNi yana tafiya zan zo masa ina gaggawa". - 4 ملاحظة
عربي Turanci urdu
18. : :
عربي Turanci urdu
19. : :
عربي Turanci urdu
20. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana ƙoƙari a cikin goman ƙarshe irin ƙoƙarin da ba ya yi a cikin waninsa.
عربي Turanci urdu
21. Mun kasance muna shirya wa Manzon Allah - Salati da amincin Allah su tabbata a gare shi - kayan aikin sa da tsarkake shi, saboda haka Allah zai aiko masa da duk abin da yake son ya aiko daga dare, don haka sai ya sa su daidai, ya yi alwala ya yi sallah.
عربي Turanci urdu
22. "Wani bawa ba zai suturta wani bawa a duniya ba sai Allah Ya suturta shi a ranar Alƙiyama".
عربي Turanci urdu
23. "Lallai kada ɗayanku ya mutu sai yana kyautatawa Allah zato".
عربي Turanci urdu
24. Cewa wani mutum ya ce: Ya manzon Allah, ina da wasu 'yan uwa ina sadar musu (da zumunci), su kuma suna yanke mini, ina kyautata musu, su suna munanawa a gareni, ina haƙuri da su, su kuma suna yi min wauta, sai ya ce: @"Idan ka kasance kamar yadda ka faɗa, to, kamar kana cusa musu toka mai zafi ne a bakin su, kuma wani mai rinjaye a kansu daga Allah ba zai gushe tare da kai ba muddin dai ka kasance a kan haka".
عربي Turanci urdu
25. "Diga-digan wani bawa ba su taɓa ƙura a cikin tafarkin Allah ba, kuma wuta ta shafe shi".
عربي Turanci urdu
26. "Babu wasu mutane da suke tashi daga wani wurin zaman da ba sa ambaton Allah a cikinsa, face sun tashi kamar mushen jaki, kuma suna masu asara".
عربي Turanci urdu
27. "Misalin wanda yake ambatan Ubangijinsa da wanda ba ya ambatan Ubangijinsa, kamar rayayye ne da matacce"*, lafazin Muslim kuma: "Misalin gidan da ake ambatan Allah a cikinsa, da gidan da ba'a ambatan Allah a cikinsa, kamar rayayye ne da matacce".
عربي Turanci urdu
28. Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zauna wata rana akan minbari muma muka zauna a gefensa, sai ya ce: @"Lallai ni ina jiye muku tsoro a baya na, abinda za'a buɗe muku na ƙawar duniya da adonta"* sai wani mutum ya ce: Ya Manzon Allah, shin alheri yana zuwa da sharri ne? sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi shiru, sai akace masa: Meke damunka ne? kana yi wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - kuma bai kulaka ba ? sai mukaga cewa can ana saukar me (da wahayi) ne? ya ce: Sai ya shafe gumi daga gare shi , sai ya ce: "Ina mai tambaya?" kamar shi ya yabe shi , sai ya ce: "Lallai alheri ba ya zuwa da sharri, yana daga abinda kaka take tsirarwa (akwai) abinda yake kashewa ko ya aibata, sai masu cin ciyayi, sun ci har saida kwiɓinansu suka cika sai suka fuskanci idan rana, sai suka yi toroso suka yi fitsari, suka yi kiwo, lallai wannan dukiyar koriyace mai zaƙi, madalla da na musulmi abinda aka bawa miskini daga gareta da maraya da ɗan matafiyi - ko kamar yadda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata ya ce -: Kuma cewa shi wanda ya ɗauketa ba tare da haƙƙinta ba, to kwatankwacinsa kamar wanda yake ci ne ba ya ƙoshi, zata zama mai yi masa shaida ranar alƙiyama". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
29. "Wanda yake son Allah Ya tseratar da shi daga baƙin cikin ranar Alƙiyama, to, ya yaye wa wanda yake cikin wani mawuyacin hali, ko ya sarayar masa (wani haƙƙi ko nauyin da ya ke kansa)".
عربي Turanci urdu
30. "Lallai cewa mafi sauƙin 'yan wuta a azaba wanda yake da takalma biyu da igiyoyi na wuta, ƙwaƙwalwarsa tana tafarfasa kamar yadda (tukunyar) tagulla take tafarfasa, ba ya ganin cewa wani mutum ya fi shi tsananin azaba, kuma shi shi ne mafi sauƙin azabarsu"
عربي Turanci urdu
31. "Za'a kusanto da mumini ranar alƙiyama daga Ubangijinsa - Mai girma da ɗaukaka - har sai ya sanya kiyayewarSa, sai Ya tabbatar masa da zunubansa*, sai Ya ce: Shin kana sane ? sai ya ce: Eh ya Ubangiji ina sani, ya ce: Lallai cewa Ni haƙiƙa Na suturtasu gareka a duniya, kuma cewa lallai Ni Zan gafarta maka su a yau, sai a ba shi takardar kyawawan ayyukansa, amma kafirai da munafukai, sai a kirasu akan kawunan halittu waɗannan sune waɗanda suka yi wa Allah ƙarya".
عربي Turanci urdu
32. Ka Guji Duniya Sai Allah ya so ka, ka guji abin hannun Mutane sai Mutane su so ka
عربي Turanci urdu
33. Na tambayi Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - daga aikin alheri da kuma zunubi, sai ya ce: @"Aikin alheri (shi ne) kyakkyawar ɗabi'a, zunubi kuma abinda ya sosu a cikin ƙirji, kuma kaƙi mutane su yi tsinkaye akansa".
عربي Turanci urdu
34. Za a shigar da Jahannama a wannan rana a kansa saboda iyayengiji dubu saba'in, tare da kowace sarauta ta sarakuna dubu saba'in da suke jan ta - 1 ملاحظة
عربي Turanci urdu
35. Mun kasance muna zaune a gefen manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, a tare damu akwai Abubakar, da Umar a cikin wasu mutane, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya miƙe a tsakaninmu, sai ya ɗan jikirta mana, sai muka ji tsoron a cutar da shi ba mu sani ba, sai muka firgita, sai muka tashi, na kasance farkon wanda ya firgita, sai na fita ina neman manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - har na zo wani shinge na mutanen Madina na Banu Najjar, sai na kewaye shi shin zan samu wata ƙofa gare shi ? ban samu ba, sai ga wata 'yar ƙorama tana shiga a cikin shingen daga rijiyar Kharija - rabi'u shi ne korama - sai na takure, sai na shiga wurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbat agare shi -, sai ya ce: "Abu Huraira" sai na ce: Eh, ya manzon Allah, ya ce: "Meke tafe da kai?" na ce: Ka kasance a tsakaninmu, sai ka miƙe, sai ka jinkirta gare mu, sai muka ji tsoron a cutar da kai bamu sani ba, sai muka firgita, sai na zama farkon wanda ya firgita, sai na zo wannan shingen, sai na takure kamar yadda dila yake takurewa, alhali waɗannan mutanen suna bayana, sai ya ce: "Ya Abu Huraira" sai ya bani takalmansa, ya ce: @"Ka tafi da takalman nan waɗannan, duk wanda ka gamu da shi ta bayan wannan shingen yana shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma zuciyarsa tana sakankancewa da ita, to ka yi masa albishir da aljanna"*, sai Umar ya zama farkon wanda ya haɗu da ni, sai ya ce: Waɗannan takalman fa ya Abu Huraira? sai na ce: Waɗannan takalman manzon Allah ne - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, ya aikoni da su cewa wanda na haɗu da shi yana shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah zuciyarsa tana mai sakankancewa da ita, in yi masa albishir da aljanna, sai Umar ya daki tsakanin nonuwana da hannunsa sai na faɗi ta bayana, sai ya ce: Ka koma ya Abu Huraira, sai na koma wurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai na fara shesseƙin kuka, kuma Umar ya hauni, sai gashi a bayana, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Meke damunka ya Abu Huraira?" na ce: Na hadu da Umar, sai na ba shi labarin abinda ka aikoni da shi, sai ya daki tsakanin nonuwana duka da na fadi ta bayana, ya ce: Ka koma, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ya Umar, me yasa ka aikata haka?" ya ce: Ya Manzon Allah, fansarka babana da babata, shin ka aiki Abu Huraira da takalmanka cewa idan ya gamu da wanda ya shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah zuciyarsa tana mai sakankancewa da ita ya yi masa albishir da aljanna? ya ce: Eh, ya ce: Kada ka aikata, domin cewa ni ina jin tsoron mutane su dogara a kanta, kyalesu su yi aiki, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: to ka kyalesu.
عربي Turanci urdu
36. "Gangaran a karatun Alƙur'ani yana tare da manyan mala'iku masu biyayya ga Allah, kuma wanda yake karanta Alƙur'ani kuma yake guragura a cikinsa yana mai shan wuya to yana da lada biyu. - 10 ملاحظة
عربي Turanci urdu
37. Baka ga Wasu Ayoyi da aka saukar da su ba a wannan Daren ba'a tava ganinsu ba? Falaqi da Nasi
عربي Turanci urdu
38. Lokuta uku Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana hana mu yin salla a cikinsu, ko binne mamatanmu a cikinsu*: Lokacin da rana ta fito a bayyane har sai ta ɗaga, da kuma lokacin da ta tsaya a tsakiyar sama har sai ranar ta karkace, da kuma lokacin da ranar ta kusa faɗuwa har sai ta faɗi.
عربي Turanci urdu
39. Allah baya karvar Sallar Wacce ta isa Haila sai da Hijabi - 1 ملاحظة
عربي Turanci urdu
40. . :
عربي Turanci urdu
41. Kuna yin hamma yayin sallah daga Shaidan, don haka idan wani daga cikinku yayi hamma, to, ya bar shi gwargwadon iyawarsa
عربي Turanci urdu
42. "Duk mutumin da ya halarci (yaƙin) Badar da Hudaibiyya ba zai shiga wuta ba".
عربي Turanci urdu
43. "Lallai cewa idan ɗayanku ya mutu za’a bijiro masa da mazauninsa safiya da maraice*, idan ya kasance daga cikin 'yan aljanna ne to yana daga cikin 'yan aljanna, idan ya kasance daga cikin 'yan wuta to yana daga cikin 'yan wuta, sai a ce: Wannan mazauninka ne har sai Allah Ya tasheka ranar alƙiyama".
عربي Turanci urdu
44. "Sallar jam'i ta fi sallar ɗayanku shi kaɗai, da yanki ashirin da biyar, kuma mala'ikun dare da mala'ikun rana suna taruwa a sallar Asuba"* Sannan Abu Huraira ya ce: Idan kun so ku karanta: {Lallai karatun alfijir (sallar Asuba) ya kasance abin halartowar (mala'iku) ne} [al-Isra'i: 78].
عربي Turanci urdu
45. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya la'anci mai yin ƙarin gashi da wacce ta nemi a yi mata ƙarin gashi, da mai yin zane a jiki da wacce ta nemi a yi mata.
عربي Turanci urdu
46. : - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
47. "Wanda ya yi azumin wani yini a tafarkin Allah, Allah Zai nisantar da fuskarsa daga wuta (tsawon) shekara saba'in".
عربي Turanci urdu
48. "Mutane ba zasu gushe ba cikin alheri matuƙar sun gaggauta buɗa baki".
عربي Turanci urdu
49. Mun kasance muna fitar da zakkar fidda kai lokacin da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana cikinmu, daga kowane ƙaramin (yaro) da babba, ɗa ne ko bawa, Sa’i na abinci, ko Sa’i na cukwi, ko Sa’i na sha'ir, ko Sa’i na dabino, ko Sa’i na zabibi*, kuma bamu gushe ba muna fitar da shi har saida Mu'awiya ɗan Abu Sufyan - Allah Ya yarda da shi - ya gabato gurinmu yana mai aikin Hajji, ko yana mai Umarah sai ya yi wa mutane magana akan minbari, ya kasance daga abinda ya yi wa mutane magana da shi cewa ya ce: Lallai ni na ga cewa mudu biyu na alkamar Sham, sun yi daidai da sa'i ɗaya na dabino, sai mutane suka yi riko da hakan, Abu sa'id ya ce: Ammma ni ba zan gushe ba ina fitar da shi kamar yadda na kasance ina fitar da shi, muddin dai na rayu har abada.
عربي Turanci urdu
50. : :
عربي Turanci urdu
51. Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana i'itikafin goman ƙarshe na Ramadan, har Ya koma ga Allah , sannan matansa suka yi i'itikafi a bayansa.
عربي Turanci urdu
52. "Ku yi sahur, domin lallai cewa akawai albarka a cikin sahur". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
53. "Kada ku gabaci Ramadan da azimin yini ko yini biyu sai dai mutumin da ya kasance yana yin wani azimi to ya azimce shi".
عربي Turanci urdu
54. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya wajabta zakkar fidda kai, Sa'i na dabino, ko Sa'i na alkama, akan bawa da ɗa, namiji da mace, ƙarami da babba cikin musulmai, kuma ya yi umarni a bada ita kafin fitar mutane zuwa sallah.
عربي Turanci urdu
55. "Ba ya halatta ga wata mace musulma ta yi tafiyar dare (ɗaya) sai a tare da ita akwai namiji muharraminta".
عربي Turanci urdu
56. "Wanda ya manta alhali yana azumi, sai ya ci ko ya sha, to ya cike aziminsa, kaɗai Allah ne Ya ciyar da shi kuma Ya shayar da shi".
عربي Turanci urdu
57. : :
عربي Turanci urdu
58. :
عربي Turanci urdu
59. "Ku yi kirdadon daren Lailatul-ƙadri a cikin mara daga goman ƙarshe na Ramadan".
عربي Turanci urdu
60. Cewa wasu mazaje daga sahabban Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - an nuna musu daren Lailatul-ƙadr a cikin mafarki a bakwan ƙarshe, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: @"Ina ganin mafarkenku haƙiƙa sun haɗu a bakwan ƙarshe, duk wanda ya kasance zai yi kardadonsa to ya yi kardadonsa a bakwan ƙarshe".
عربي Turanci urdu
61. Cewa wasu mutane daga sahabban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sun ce wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Ya Manzon Allah, masu dukiyoyi sun tafi da ladaddaki, suna yin sallah kamar yadda muke yin sallah, suna azimi kamar yadda muke yin azimi, kuma suna yin sadaka da ragowar dukiyoyinsu, ya ce: @"Shin yanzu haƙiƙa Allah Bai sanya muku abinda zaku dinga sadaka dashi ba? lallai dukkan tasbihi sadaka ne, dukkan kabbara sadaka ce, dukkan tahmidi sadaka ce, dukkan hailala sadaka ce, horo da aikin alheri sadaka ne, kuma hani daga abin ƙi sadaka ne, a cikin tsokar ɗayanku ma sadaka ne"*, Suka ce: Ya Manzon Allah, shin ɗayanmu zai zo wa sha'awarsa kuma ya zama yana da lada a cikinta? ya ce: "Shin kuna ganin da ace zai sanyata a cikin haram shin zai zama a kansa akwai zunubi a cikinsa? to haka nan idan ya sanyata a cikin halal zai zama yana da lada".
عربي Turanci urdu
62. "Wanda ya yayewa wani mumini wani baƙin ciki daga baƙin cikin duniya Allah Zai yaye masa wani baƙin ciki daga baƙin cikin ranar alƙiyama*, wanda ya yalwatawa wanda yake cikin matsuwa to Allah Zai yalwata masa a duniya da lahira, wanda ya suturta wani musulmi Allah Zai suturta shi a duniya da lahira, Allah Yana cikin taimakon bawa matuƙar bawan yana cikin taimakon ɗan'uwansa, wanda ya bi wata hanya yana neman Ilimi a cikinta to Allah Zai sawwaƙe masa hanyar shiga aljanna da ita, kuma wasu mutane basu taru ba a wani ɗaki daga cikin ɗakunan Allah suna karanta littafin Allah kuma suna dirasarsa a tsakaninsu sai nutsuwa ta saukar musu, kuma rahama ta lullubesu, mala'iku sun kewayesu, kuma Allah Ya ambacesu a cikin wadanda ke tare da shi, wanda aikinsa ya jinkirtar da shi to nasabarsa bazata gaggauto da shi ba".
عربي Turanci urdu
63. "Ya ku mutane, ku tuba zuwa ga Allah, lallai cewa ni ina tuba zuwa gareShi a yini sau ɗari". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
64. Abu Musa ya yi ciwo ciwo mai tsanani, sai ya suma alhali kansa yana cikin ɗakin wata mata daga iyalansa, bai samu damar da zai dawo mata da komai ba, lokacin da ya farka, ya ce: Ni na kuɓuta (na barranta) daga wanda Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kuɓuta da shi, @Lallai cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kuɓuta daga mai ɗaga murya da mai aske kanta da mai tsaga kayanta.
عربي Turanci urdu
65. "Banu Isra'il sun kasance Annabawa ne suke shugabantarsu, duk lokacin da wani Annabi ya rasu sai wani Annabin ya maye gurbinsa, lallai cewa babu wani Annabi a baya na, za'a samu halifofi zasu yawaita*" Suka ce: Da me zaka umarce mu? ya ce: "Ku cika caffar na farko sai na farko, ku basu haƙƙinsu, domin cewa Allah Mai tambayarsu ne daga abinda Ya basu kiwo".
عربي Turanci urdu
66. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan goman ƙarshe ta shiga zai raya dare, zai farkar da iyalansa, zai yi ƙoƙari zai ɗaure gwabso.
عربي Turanci urdu
67. "Ibada a cikin rashin zaman lafiya kamar hijira ce zuwa gareni".
عربي Turanci urdu
68. : . : :
عربي Turanci urdu
69. :
عربي Turanci urdu
70. : : :
عربي Turanci urdu
71. "Idan ɗayanku zai yi hamma to ya riƙe bakainsa da hannunsa, domin cewa Shaiɗan yana shiga".
عربي Turanci urdu
72. : : - 4 ملاحظة
عربي Turanci urdu
73. "Allah ba Ya duba zuwa wanda ya ja tufansa (ƙasa) dan girman kai".
عربي Turanci urdu
74. : :
عربي Turanci urdu
75. :
عربي Turanci urdu
76. : - 8 ملاحظة
عربي Turanci urdu
77. "Lallai masu yawaita tsinuwa ba sa zama masu shaida ko masu ceto a ranar alƙiyama".
عربي Turanci urdu
78. "Lalle Ubangijinku Mai kunya ne kuma Mai karamci ne, Yana jin kunyar bawanSa idan ya ɗaga hannayensa zuwa gare Shi Ya dawo da su babu komai".
عربي Turanci urdu
79. "Wasu mutane basu zauna a wani wurin zama ba basu ambaci Allah a cikinsa ba kuma ba su yi salati ga Annabinsu ba sai hasara ta kasance a kansu, idan (Allah) Ya so Ya azabtar da su idan kuma Ya so Ya gafarta musu".
عربي Turanci urdu
80. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana son Addu'ar da ta tattaro komai, kuma yana ƙyale wacce ba ita ba.
عربي Turanci urdu
81. "Rantsuwa mai sa anfani ce a haja (kayan sayarwa), kuma mai shafe albarkar riba ce".
عربي Turanci urdu
82. :
عربي Turanci urdu
83. : - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
84. "An turbuɗe hancin mutumin da aka ambaceni a wurinsa bai yi mini salati ba, an turbuɗe hancin mutumin da Ramadan ya shiga sannan ya fita ba’a gafarta masa ba, kuma an turbuɗe hancin mutumin da mahaifansa suka tsufa a wurinsa amma basu shigar da shi aljanna ba".
عربي Turanci urdu
85. "Lallai kai kana azimi tsawon shekara, kuma kana tsayuwar dare?", sai na ce: Eh, ya ce: "Lallai kai idan ka aikata hakan ido zai yi rauni saboda shi, kuma zuciya zata gajiya saboda hakan, @Wanda ya azimci zamani (a here) to bai yi azimi ba, azimin kwana uku azimin zamani ne gaba ɗayansa"*, sai na ce: Lallai cewa ni zan iya sama da hakan, ya ce: "To ka yi azimin (Annabi) Dawud - aminci ya tabbata agare shi -, ya kasance yana azimtar yini kuma ya sha yini, kuma ba ya gudu idan ya gamu da maƙiya".
عربي Turanci urdu
86. Cewa wasu mutane daga sahabban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sun tambayi matan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - game da aikinsa a ɓoye? sai sashinsu ya ce: Ba zan auri mata ba, sashinsu kuma ya ce: Ba zan ci nama ba, sashinsu ya ce: Ba zan yi bacci akan shinfiɗa ba, sai ya godewa Allah kuma ya yi yabo gare shi, sai ya ce: @"Me ya samu wasu mutane ne sun ce kaza da kaza? sai dai cewa ni ina sallah kuma ina bacci, ina azimi ina buɗe baki, kuma ina auren mata, wanda ya ƙi sunnata to ba ya tare da ni".
عربي Turanci urdu
87. "Babu wasu musulmai biyu da zasu haɗu sannan su gaisa hannu da hannu sai an gafarta musu kafin su rabu". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
88. . :
عربي Turanci urdu
89. :
عربي Turanci urdu
90. "Lallai cewa zukatan 'ya'yan Adam dukkansu (suna) tsakanin yatsu biyu daga yatsun (Ubangiji) al-Rahman, kamar zuciya ɗaya, yana jujjuyata yadda Ya so"* sannan tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Ya Allah Ya mai jujjuya zukata Ka juya zukatanmu a kan biyayyarKa". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
91. Ba'a taɓa ba wa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zabi ba tsakanin abubuwa biyu face sai ya zaɓi mafi sauƙinsu, matuƙar bai kasance saɓo ba, idan ya kasance saɓo ne to ya kasance ya fi kowa nisantar shi*, kuma Annabi bai bai taɓa ramuwar gayya ga kansa ba ko sau ɗaya, sai dai idan an keta hurumin Allah, sai ya yi hukunci saboda Allah da ita.
عربي Turanci urdu
92. "Allah Ya ni'imtar da mutumin da ya ji wani abu daga gurimmu sai ya isar da shi kamar yadda ya ji, da yawa wanda aka isarwa yana zama mafi kiyayewa daga wanda ya ji".
عربي Turanci urdu
93. "Ni ne shugaban mutane a ranar alƙiyama, shin kun san daga menene hakan? @Allah Zai tara mutane na farko da na ƙarshe a bigire ɗaya, mai kira zai jiyar da su kuma gani zai ƙetare su, rana zata kusanto, sai baƙin ciki da takaici ya kai ga mutane abinda ba za su iya ɗauka ba, kuma ba za su iya jurewa ba*, sai mutane su ce: Shin bakwa ganin abinda haƙiƙa ya kai muku ? shin bakwa duba wanda zai yi muku ceto zuwa ga Ubangijinku ba? sai wasu daga mutane su ce wa wasu: Ku je gurin (annabi) Adam, sai su zo wa Adam - aminci ya tabbata agare shi - sai su ce masa: Kai ne uban mutane, Allah Ya halicceka da hannunSa, kuma Ya busa maka daga ranSa, kuma Ya umarci mala'iku sai suka yi maka sujjada, ka nema mana ceto ga Ubangijinka, shin baka ganin abinda muke cikinsa, shin baka gani zuwa abinda ya kai mana? sai Adam ya ce: Lallai Ubangijina hakika Ya yi fushi a yau bai taba irin wannan fushin ba, kuma ba zai taba yin irin wannan fushin ba, kuma lallai ni hakika Ya hanani daga bishiya sai na saba maSa, kaina kaina kaina, ku tafi zuwa wanina, ku tafi zuwa (annabi) Nuhu. Sai su zo wa (annabi) Nuhu sai su ce: kai Nuhu, lallai kai ne farkon manzanni zuwa mutanen kasa, hakika Allah Ya ambaceka bawa mai yawan godiya, shin baka ganin abinda muke cikinsa, shin baka gani zuwa abinda ya kai mana, shin baka nema mana ceto ga Ubangijinka ba? sai ya ce: Lallai Ubangijina Ya yi fushi a yau bai taba fushi irinsa ba, kuma ba zai yi fushi a bayansa ba, kuma lallai cewa ni akwai mummunar addu'ar da na yi akan mutanena, kaina kaina kaina, ku tafi zuwa wanina, ku tafi gurin (annabi) Ibrahim. Sai su zo wa (annabi) Ibrahim sai su ce: kai Ibrahim, kai ne Annabin Allah kuma badaɗayinSa daga mutanen ƙasa, ka nema mana ceto ga Ubangijinka, shin baka ganin abinda muke cikinsa? sai ya ce musu: Lallai Ubangijina haƙiƙa Ya yi fushi a yau fushin da bai taɓa fushi irinsa ba, kuma ba zai yi fushi a bayansa ba irinsa, lallai cewa ni na yi ƙarya sau uku, kaina kaina kaina, ku tafi zuwa wanina, ku tafi zuwa ga (annabi) Musa. Sai su zo wa (annabi) Musa sai su ce: Kai Musa kaine Manzon Allah, Allah Ya fifitaka da saƙonninSa da kuma zancenSa akan mutane, ka nema mana ceto ga Ubangijnka, shin baka ganin abinda muke cikinsa? sai ya ce: Lallai Ubangijina hakika Ya yi fushin da bai taba fushi irinsa ba, kuma ba zai yi fushi a bayansa irinsa ba, lallai ni naa kashe wani rai da ba'a yi umarni da in kasheta ba, kaina kaina kaina, ku tafi zuwa wanina, ku tafi zuwa (annabi) Isa. Sai su zo wa (annabi) Isa sai su ce: kai Isa, kaine Manzon Allah kuma kalmarSa da ya jefata zuwa Maryam kuma rai daga gareShi, kuma ka yi wa mutane magana a cikin shinfidar goyo, ka nema mana ceto ga Ubangijinka, shin baka ganin abinda muke cikinsa? sai Isa ya ce: Lallai Ubangijina hakika Ya yi fushin da bai taba fushi irinsa ba, kuma ba zai yi fushi a bayansa irinsa ba, ba zai anbaci wani zunubi ba, kaina kaina kaina, ku tafi zuwa wanina, ku tafi zuwa (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -". Sai su zo wa (annabi) Muhammad sai su ce kai ne Manzon Allah kuma cika makin Annabawa, hakika Allah Ya gafarta maka abinda ya gabata daga zunubinka da abinda ya jinkirta, ka nema mana ceto zuwa ga Ubangijinka, shin baka ganin abinda muke cikinsa? sai in tafi, sai in zo ƙarƙashin al’arshi sai infaɗi ina mai sujjada ga Ubangina, sannan Allah Ya buɗe mini daga godiyarSa da kyakkyawan yabo gareShi na wani abinda bai taɓa buɗewa wani a gabani na ba, sannan a ce: Ya Muhammad ka ɗago kanka, ka yi tambaya za'a baka shi, ka nemi ceto za'a baka ceto, sai in dago kaina, sai in ce: Al'ummata ya Ubangiji, al'ummata ya Ubangiji, al'ummata ya Uabngiji, sai ace: Ya Muhammad ka shigar daga al'ummarka wadanda babu wani hisabi akansu ta kofar dama daga kofofin aljanna, kuma su suna tarayya da mutane a koma bayan haka na kofofi". sannan ya ce: "Na rantse da wanda raina yake a hannunSa, lalai tsakanin ginshikai biyu daga ginshikan aljanna kamar tsakanin Makka ne da Hajar, ko tsakanin Makka ne da Busra".
عربي Turanci urdu
94. "Lallai mumini yana da wata shema a cikin aljanna ta lu'ulu'u ɗaya mai ƙofa a cikinta, tsawonta mil sittin ne, mumini yana da mata a cikinta, mumini zai kewayesu amma sashinsu ba zai ga sashi ba".
عربي Turanci urdu
95. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tsinewa namijin da ya sanya kayan mace, da macen da ta sanya kayan namiji.
عربي Turanci urdu
96. "Wanda ya kasance yana da abin yankan da zai yanks shi (na Layya) to idan jijirin watan Zul-Hijja ya kama, to kada ya cire wani abu daga gashinsa ko faratansa har sai ya yi layya".
عربي Turanci urdu
97. "Idan (watan) Ramadan ya zo sai a buɗe ƙofofin aljanna, kuma a kukkule ƙofofin wuta, a ɗaɗɗaure shaiɗanu".
عربي Turanci urdu