عَنْ أُبَيِّ بْنِ كَعْبٍ رضي الله عنه قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:

«لاَ تَسُبُّوا الرِّيحَ، فَإِذَا رَأَيْتُمْ مَا تَكْرَهُونَ فَقُولُوا: اللَّهُمَّ إِنَّا نَسْأَلُكَ مِنْ خَيْرِ هَذِهِ الرِّيحِ وَخَيْرِ مَا فِيهَا وَخَيْرِ مَا أُمِرَتْ بِهِ، وَنَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ هَذِهِ الرِّيحِ وَشَرِّ مَا فِيهَا وَشَرِّ مَا أُمِرَتْ بِهِ».
[صحيح] - [رواه الترمذي]
المزيــد ...

Daga Ubaiyu Dan Ka'ab -Allah ya yarda da shi- zuwa ga Annabi: "Kada ku kuskura ku Zagi Iska, idan kuka ga abinda bakwa so to kuce: Ya Ubangiji Muna rokonka daga Alkairin wannan Iskar, da kuma Alkairin abinda ya ke cikinta, da kuma Alkairin da aka Umarce ta da shi, kuma muna neman tsari da kai daga Sharrin wannan Iskar, da kuma Sharrin abinda yake cikinta, da kuma Sharrin abinda aka Umarce ta da shi"
Ingantacce ne - Al-Tirmithi Ya Rawaito shi

Bayani

Annabi ya hana Zagin Iska; domin ita ma abar halitta ce kuma umarnin Allah take bi, to zagin ta zagin Allah ne, da kuma fushi da abinda ya hukunta, sannan Annabi ya shiryar zuwa ga Mahaliccinta da rokonsa daga Alkairinta da kuma tsari daga Sharrinta; sabida abinda yake cikinta na Bautar Allah, kuma hakan shi ne halin masu kadaita Allah

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin

Ma"anonin Kalmomi