Karkasawa:
عَنْ أَبِي عُبَيْدٍ، مَوْلَى ابْنِ أَزْهَرَ، قَالَ:

شَهِدْتُ العِيدَ مَعَ عُمَرَ بْنِ الخَطَّابِ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ، فَقَالَ: هَذَانِ يَوْمَانِ نَهَى رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ عَنْ صِيَامِهِمَا: يَوْمُ فِطْرِكُمْ مِنْ صِيَامِكُمْ، وَاليَوْمُ الآخَرُ تَأْكُلُونَ فِيهِ مِنْ نُسُكِكُمْ.
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abu Ubaida Baron Dan Azhar ya ce : Mun halarci Idi tare da Umar Dan Khaddab - Allah ya yarda da shi - sai ya ce: "wadan nan kwanaki biyu Mazon Allah - Tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi - ya hana Azuminsu : Ranar Buda bakinku daga Ramadan dinku, Rana ta biyun : Ranar da kuke ci daga layyarku.
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Allah Madaukaki ya sanya kwanaki biyu su zama Idi ga Musulmi , kuma kowanne daga cikinsu yana hade da wata Ibada, sabida ranar Karamar Sallah tana hade da cikar Azumi, domin wajibi ne akan kowane Musulmi ya sha ruwaa wannan rana don godiya ga Allah da kuma cikar Ni'amar Azumi da kuma bayyanar da Ni'amar bude baki wacce Allah ya umarce su da ita bayan Azumi Allah yana cewa: "Kuma don ku cika lokaci kuma ku girmama Allah sabida abinda ya shirye ku da shi kuma sai ku gode masa" kuma rana ta biyu ita ce ranar Babbar Sallahkuma itama tana hade da Ibadar Hadaya da kuma layya, sabida Mutane sunayin Hadaya da Layya kuma suna bayyana Ibadar Allah da cin Abinci da kuma shan Abin sha daga cikin hakan ya wajaba akan Musulmi buda baki a wadan nan kwanaki kuma haramun ne Azumi acikinsu

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin

Ma"anonin Kalmomi

kashe kashe
Kari