kase kashen kana nan rassa

lis din Hadisai

1. "Ku barni a abinda na bar muku, kaɗai waɗanda ke gabaninku sun halaka ne da tambayarsu da kuma saɓawarsu ga annabawansu*, idan na haneku daga wani abu to ku nuisance shi, idan na umarceku da wani abu to ku zo da shi daidai ikonku".
عربي Turanci urdu
2. "Wanda aka haramtawa sauƙi to an haramta masa alheri".
عربي Turanci urdu
3. "Na hore ku da gaskiya, saboda gaskiya tana shiryarwa zuwa ga aikin alheri, kuma lallai aikin alheri yana shiryarwa zuwa ga Aljanna*, kuma mutum ba zai gushe ba yana yin gaskiya, kuma yana kirdadon gaskiya har sai an rubuta shi a wajen Allah mai yawan gaskiya ne. Kuma na haneku da ƙarya, saboda ƙarya tana shiryarwa ne zuwa ga fajirci, kuma fajirci yana shiryarwa ne zuwa ga wuta, mutum ba zai gushe ba yana yin ƙarya kuma yana kirdadon ƙarya har sai an rubuta shi a wajen Allah mai yawan ƙarya". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
4. : :
عربي Turanci urdu
5. Manzon Allah SAW ya Kasance yana E'itikafi a cikin goman kowane Azumin Ramadan, to yayin da shekarar da aka karbi ransa ta zo yayi E'itikafi kwana Ashirin
عربي Turanci urdu
6. An tambayi manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - game da mutumin da yake yaƙi dan jarumta, (da wanda) yake yaƙi dan ƙabilanci, (da wanda) yake yaƙi dan riya, wanne ne saboda Allah? sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: @"Wanda ya yi yaƙi dan kalmar Allah ta zama maɗaukakiya, to shi ne sabo da Allah".
عربي Turanci urdu
7. "Kar ku sanya alhariri (siririnsa) ko dibaji, kuma kar ku sha a cikin kofi na zinare ko na azurfa, haka nan kar ku ci a cikin farantansu, don kuwa na su ne (wanda ba muslmi) a nan duniya ku kuma zaku yi amfani da su a lahira".
عربي Turanci urdu
8. Lallai cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fito ga wata halƙa daga sahabbansa, sai ya ce; "Me ya zaunar da ku?" suka ce: Mun zauna muna ambatan Allah muna gode masa akan abinda ya shiryar da mu na musulunci, kuma ya yi baiwa da shi garemu, ya ce: "Kun rantse da Allah babu abinda ya zaunar da ku sai hakan? suka ce: Wallahi babu abinda ya zaunar da mu sai hakan, ya ce: @"Amma ni ban rantsar da ku ba dan tuhuma gareku, sai dai cewa (Mala'ika) Jibril ya zo min sai ya ba ni labarin cewa Allah - mai girma da ɗaukaka - Yana yi wa mala'iku alfahari da ku".
عربي Turanci urdu
9. "ku daidaita sahunku, don daidaita shahu na daga cikar sallah". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
10. "Kada wani mumini ya ki wata mumina, in ya ki wata ɗabi’ar daga gareta to zai so wata ɗabi’ar daga gareta* Ko ya ce: "Waninsa".
عربي Turanci urdu
11. "Idan kun zo wa bayan gida to kada ku fuskanci alƙibla, kuma kada ku juya mata baya sai dai ku fuskanci gabas ko ku fuskanci yamma"* Abu Ayyub ya ce: Sai muka je Sham sai muka samu banɗakuna an gina su ɓangaren alƙibla sai mu juya, muka nemi gafarar Allah - Maɗaukakin sarki -".
عربي Turanci urdu
12. "Kada ɗayanku ya kuskura ya taɓa azzakarinsa da damansa, a halin yana fitsari, kuma kada ya yi tsarki na bayan gida da damansa, ko kuma ya yi nunfashi a ƙwarya".
عربي Turanci urdu
13. Cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana ɗaga hannayensa daura da kafaɗunsa in zai fara sallah,* haka nan in zai yi kabbara dan ruku'u, haka idan kuma zai ɗago kansa daga ruku'u sai ya ɗagasu, kuma ya ce: "Allah Ya ji wanda ya gode maSa, ya Ubangijinmu godiya ta tabbata gare ka, ya kasance ba ya yin haka a cikin sujjada.
عربي Turanci urdu
14. Manzon Allah - tsira da aminci su tabbata a gare shi - ya kasance idan ya yi kabbara a sallah, sai ya yi shiru ɗan wani lokaci gabanin fara karatu, sai na ce: Ya manzon Allah, fansarka baba na da Baba ta, kana ganin shirun da kake yi tsakanin kabbara da karatu, me kake cewa? ya ce: Ina cewa: @Ya Allah Ka nesanta tsakanina da kurakurai na kamar yadda Ka nesanta tsakanin mahudar rana da mafaɗarta*, Ya Allah Ka tsaftace ni daga zunubaina kamar yadda ake tsaftace farar tufa daga datti. Ya Allah Ka wanke ni daga zunubai na da ruwan ƙanƙara kuma mai tsananin sanyi".
عربي Turanci urdu
15. "Shin bana ba ku labari ba game da Jujal, wanda babu wani annabi da ya zantar da mutanensa shi ? lallai shi mai ido ɗaya ne, kuma shi zai zo a tare da shi akwai kwatankwacin aljanna da wuta,* wacce zai ce ita ce aljanna to ita ce wuta, lallai ni ina gargaɗarku kamar yadda (Annabi) Nuhu ya gargaɗi al'ummarsa da shi".
عربي Turanci urdu
16. Ku daidaita a cikin sujjada, kar ku shimfida zira'oinku irin yadda kare ke shimfida nasa.
عربي Turanci urdu
17. "Kaɗai kwatankwacin abokin zama na gari da mummunan abokin zama, kamar maɗaukin almiskine da mai busa zugazugi,* maɗaukin alimiski: Kodai ya baka, ko kuma ka saya daga gare shi, ko kuma ka samu ƙanshi mai daɗi daga gare shi, mai busa zugazugi kuwa: Kodai ya ƙona kayanka, ko kuma ka samu mummunan ƙanshi daga gare shi". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
18. "Ku yi gaggawa da ayyuka (na alheri), wasu fitinu kamar yankin dare ne mai duhu,* mutum zai wayi gari yana mumini ya kai yammaci yana kafiri, ko ya yammanta yana mumini ya wayi gari yana kafiri, zai sayar da addininsa da wata haja ta duniya". - 4 ملاحظة
عربي Turanci urdu
19. Cewa annabi - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan yana sallah yana buɗa tsakanin hannayensa har sai farin hammatarsa ya bayyana.
عربي Turanci urdu
20. :
عربي Turanci urdu
21. ’’Lamarin mumini da ban mamaki yake, dukkannin al’amuransa alheri ne, kuma hakan ba ya kasancewa ga kowa sai ga mumini *,idan abin farinciki ne ya same shi sai ya gode wa Allah sai, sai ya zamar masa alheri, idan kuma na sharri ne ya same shi sai ya yi haƙuri, shi ma sai ya zamar masa alheri’’. - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
22. SIFFAR WANKAN JANABA
عربي Turanci urdu
23. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance idan zai yi atishawa, yana sanya hannunsa - ko tufafinsa - a bakinsa, kuma ya runtse - ko matse - muryarsa da shi.
عربي Turanci urdu
24. "Lallai za ku bi hanyoyin waɗanda zo kafinku, taki da taki, zira'i da zira'i*, har da ko sun shiga ramin damo ne sai kun bi su" Muka ce: Ya manzon Allah ! Yahudawa da Nasara? ya ce: "To su wa?".
عربي Turanci urdu
25. Daga kanka ka fada za'a ji, ka roka a baka, ka nemi ceto za'a baka ceton
عربي Turanci urdu
26. "Babu cuta mai yaɗuwa zuwa ga wani (da karantanta) babu canfi, ko mujiya, ko Safar, kuma ka guje wa kuturu kamar yadda kake guje wa zaki".
عربي Turanci urdu
27. "Lallai zan bai wa wani mutum wannan tutar Allah Zai yi buɗi ta hannunsa, yana son Allah da manzaonSa kuma Allah da manzonSa suna son shi". Ya ce: Sai mutane suka kwana suna tattaunawa a daran waye a cikinsu za'a ba shi ita, lokacin da mutane suka wayi gari sai suka yi jijjifi ga manzon Allah - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - kowanne su yana ƙaunar a ba shi ita, sai ya ce: "Ina Aliyu ɗan Abi Dalib?" sai aka ce : Shi ya manzon Allah yana ciwon idanu, ya ce: "Ku aike masa", sai aka zo da shi sai manzon Allah - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya yi tofi a cikin (idanuwa) ya yi masa addu'a, sai ya warke kai kace babu wani ciwo a tare da shi, sai ya ba shi tuta, sai (Sayyidina) Aliyu ya ce: Ya manzon Allah, shin zan yake su ne har sai sun zama irinmu? sai ya ce: "Ka zarce a hankali har sai ka sauka a farfajiyarsu, sannan ka kira su zuwa ga musulunci, ka ba su labari da abinda yake wajaba akansu na hakkin Allah a cikinsa,@ na rantse da Allah, Allah ya shiryar da mutum daya da kai shi ne mafi alheri daga jajayen ni'imomi (rakuma)". - 4 ملاحظة
عربي Turanci urdu
28. "Lallai mutane idan suka ga azzalumi ba su yi riƙo da hannayensa ba, ya kusa Allah Ya gamesu da uƙuba daga gare shi".
عربي Turanci urdu
29. "Shin ba na nuna muku abin da Allah Ya ke shafe kurakurai da shi ba, kuma Yake ɗaukaka darajoji da shi?*" Suka ce: Na'am, ya Manzon Allah, ya ce: "Cika alwala a lokutan da ake ƙi, da yawan takawa zuwa masallatai, da jiran sallah bayan sallah, wadannan su ne shi ne zaman dako". - 6 ملاحظة
عربي Turanci urdu
30. "Shin ba na baku labari da mafificin ayyukanku ba, kuma mafi tsarkinsu a gurin Mamallakinku, mafi ɗaukakarsu a darajojinku* kuma mafi alheri agareku daga ciyar da zinari da azirfa, kuma mafi alheri agareku daga ku haɗu da maƙiyanku ku daki wuyan su, suma su daki wuyan ku?" suka ce: Eh. Ya ce: "Ambatan Allah - Maɗaukakin sarki".
عربي Turanci urdu
31. Wani mutum daga mutanen Najad ya zo wurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - mai dattin kai, muna jin ƙarfin muryarsa, ba ma fahimtar abinda yake faɗa har ya kusanto ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai gashi yana tambaya game da musulunci, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Salloli biyar a yini da dare" sai ya ce: Shin akwai wasu kuma akaina? ya ce: "A'a, sai dai idan ka yi nafila. Da azumin Ramadan”. Sai ya ce: Shin akwai wani kuma?. sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Saidai idan ka yi na nafila. Sai ya ambata masa zakka, sai ya ce: Shin akaina akwai waninta ? ya ce: "A'a, saidai idan ka yi nafila", ya ce: Sai mutumin ya juya baya, yana cewa: Na rantse da Allah, ba zan kara akan wannan ba, kuma ba zan rage daga gare su ba, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce@ ya rabauta idan gasgata hakan".
عربي Turanci urdu
32. "Mafificin yinin da rana ta ɓullo a cikinsa yinin Juma'a*, a cikinsa ne aka halicci (Annabi) Adam, kuma a cikinsa ne aka shigar da shi aljanna, kuma a cikinsa ne aka fitar da shi daga gareta, kuma AlKiyama ba za ta tsayaba sai a ranar Juma'a".
عربي Turanci urdu
33. : :
عربي Turanci urdu
34. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana tafiya a hanyar Makka, sai ya wuce wani dutse ana ce masa Jumdan, sai ya ce: "Ku tafi ! wannan Jumdan ne,@Masu kaɗaitawa sun rigaya*" Suka ce: Suwaye musu kaɗaitawa ya manzon Allah? ya ce: "Masu ambatan Allah da yawa maza da mata masu ambatan Allah".
عربي Turanci urdu
35. Na gamu da Sauban 'yantaccen bawan Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - sai na ce: Ka ba ni labari da wani aikin da zan aikata shi Allah Ya shigar da ni Aljanna da shi? ko ya ce, na ce: Da mafi son ayyuka zuwa ga Allah, sai ya yi shiru. Sannan na tambaye shi, sai ya yi shiru, sannan na tambaye shi a karo na uku sai ya ce: Na tambayi Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - game da wannan, sai ya ce: @"Na umarce ka da yawan sujjada ga Allah, domin kai ba za ka yi wata sujjada ga Allah ba, sai Allah Ya ɗaga darajar ka da ita, kuma Ya sarayar da kuskure da ita"* Ma'adan ya ce: Sannan na gamu da Abu al-Darda'i sai na tambaye shi sai ya fada min abinda Sauban ya faɗa mini.
عربي Turanci urdu
36. "Wanda ya sallaci sanyaya biyu zai shiga aljanna". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
37. :
عربي Turanci urdu
38. "Lallai Allah ya yafewa Al-umma ta Kuskure da Mantuwa, da kuma abunda aka Tilasta musu akansa" - 1 ملاحظة
عربي Turanci urdu
39. Ku ji tsoron Allah a duk inda kuke, kuma ku bi munanan abubuwa masu kyau, ku share su, ku ƙirƙira mutane da kyawawan halaye - 4 ملاحظة
عربي Turanci urdu
40. "Lalle ne Allah - Maɗaukakin sarki - Yana shimfiɗa hannunSa da daddare domin mai laifi da rana ya tuba, kuma Yana shimfiɗa hannunSa da rana domin mai laifi da daddare ya tuba, har sai rana ta ɓullo daga yammacinta". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
41. "Kowacce gaɓa daga (jikin) mutane akwai sadaka a kanta*, kowanne yinin da rana ta fito a cikin sa da (mutum) zai daidaita tsakanin mutune biyu sadaka ne, kuma ya taimaki mutum game da dabbar sa; sai ya ɗora shi a kanta, ko ya ɗauke masa kayan sa a kanta, to, sadaka ne, kuma kalma mai daɗi sadaka ce, kuma kowanne taku da zai yi zuwa sallah sadaka ne, kuma ya kau da ƙazanta daga hanya sadaka ne".
عربي Turanci urdu
42. Jinin Mutum Musulmi Bai halatta basai da dayan abubuwa Uku : Tsoho Mazinaci , ko wanda ya kashe a kashe shi, Da Mutumin da yayi Ridda daga Addininsa ya futa daga cikin Musulmi.
عربي Turanci urdu
43. "Ɗayanku ba zai yi imani ba, har sai ya sowa ɗan uwansa abinda yake sowa kansa". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
44. Zalunci duhu ne a ranar tashin kiyama - 3 ملاحظة
عربي Turanci urdu
45. "Wanda ya yi wanka irin wankan janaba a ranar Juma`a, sannan ya tafi, kamar ya bayar da sadakar rakuma ne*, wanda ya tafi a lokaci na biyu, kamar ya bayar da sadakar saniya ne. wanda ya tafi a lokaci na uku kamar ya bayar da sadakar rago ne mai ƙaho. wanda ya tafi a lokaci na huɗu kamar ya bayar da kaza ne, wanda kuma ya tafi a lokaci na biyar kamar ya bayar da ƙwai ne. Idan liman ya fito Mala`iku za su halarto suna sauraron zikiri (Huɗuba)".
عربي Turanci urdu
46. :
عربي Turanci urdu
47. "Wanda ya yi alwala sai ya kyautata alwala sannan ya zo Juma'a sai ya saurari huduba kuma ya yi shiru za'a gafarta masa abinda ke tsakaninsa da tsakanin Juma'a da ƙarin kwanaki uku*, wanda ya taba tsakankwani to haƙiƙa ya yi yashasshiyar magana".
عربي Turanci urdu
48. Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka - ya ce:@Yakai ɗan Adam lallai cewa kai baka roƙeni ba, ka yi kwaɗayi gareni zan gafarta maka abinda ya kasance gareka babu ruwaNa*, Ya kai ɗan Adam da zunubanka sun kai ƙololuwar sama sannan ka nemi gafarata zan gafarta maka, babu ruwaNa*, Ya kai ɗan Adam lallai cewa kai da ka zo min da kurakurai cikin ƙasa sannan ka gamu dani ba yi min tarayya da wani abu ba, da na zo maka da gafara cikinta". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
49. "Ya ku mutane ku yaɗa sallama, ku ciyar da abinci, ku sadar da zumunci, ku yi sallah alhali mutane suna bacci, zaku shiga aljanna cikin aminci".
عربي Turanci urdu
50. "Lallai Addini mai sauƙi ne, babu wanda zai tsananta cikinsa face sai ya rinjaye shi, saboda haka ku daidaita ku kusanto*, ku yi bushara, ku nemi taimakon Allah da jijjifi da kuma yammaci da wani abu na duhun dare".
عربي Turanci urdu
51. An tambayi Annabi game da abu mafi yawa da yake shigar da Mutane" Al-janna? ya ce: Tsoron Allah da kyawawan Halaye, kuma aka tambaye shi game da abu mafi yawa da yake jefa Mutane wuta sai ya ce Baki da Farjin su"
عربي Turanci urdu
52. "Duk wanda yake da iko a cikinku to ya yi aure, domin cewa shi ne yafi rintse ido, kuma ya fi katange farji, wanda ba zai iya ba to na umarce shi da azimi, domin shi kariyane gare shi".
عربي Turanci urdu
53. "Mutane Uku ba zasu shiga Al-janna ba: Mashayin giya da mai yanke Zumunci, da Mai Gasgata Masu Sihiri" - 1 ملاحظة
عربي Turanci urdu
54. Kuma ai ansanya Limami ne don ayi koyi da shi, to kuma kada ku saba Masa, to idan yayi kabbara to kuyi kabbara, kuma idan yayi ruku'u to kuyi ruku'i, kuma idan yace Allah yaji mai gode masa,to ku ce: Ubangijinmu godiya ta tabbata a gareka, kuma idan yayi Sujada to kuyi Sujada, kuma idan yai Sallah a zaune to kuyi sallah kuma a a zaune baki dayanku
عربي Turanci urdu
55. Cewa Faɗima - Allah Ya yarda da ita - ta zo wajen Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - tana kawo ƙarar abinda take gamuwa da shi a hannunta na daka, kuma labari ya isar mata cewa wani bawa ya zo masa, bata same shi ba, sai ta ambaci hakan ga A'isha, lokacin da ya dawo sai A'isha ta ba shi labari, (Aliyu) ya ce: Sai ya zo mana alhali mun kwanta, sai muka tafi muka tashi, sai ya ce: "Ku zauna a wurinku" sai ya zo sai ya zauna tsakani na da ita, sai naji sanyin diga-digansa akan cikina, sai ya ce: "@Shin bana shiryar daku ga mafi alheri daga abinda kuka tambaya ba? idan kun kwanta - ko kunzo shinfiɗarku - to ku yi tasbihi sau talatin da uku, ku yi hamdala sau talatin da uku, ku yi kabbara sau talatin da da hudu, to shi ne mafi alheri gareku daga dan aiki".
عربي Turanci urdu
56. "wani Mutum yace: Ya Manzon Allah wani Mutum daga cikin mu yakan gamu da Danuwansa ko Abokinsa shin ya durkusa masa, sai ya ce to ya rikeshi ya ya sunbance shi ? sai yace aa sai ya ce to ya kama hannunsa su gaisa? ya ce: Ey" - 1 ملاحظة
عربي Turanci urdu
57. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance mafi kyauta cikin mutane, kuma ya kasance mafi kyutar da yake yi a Ramadan ne lokacin da Jibril ya haɗu da shi*, ya kasance yana haɗuwa da shi a cikin kowane dare na Ramadan sai su yi nazaran shi AlƘu'ani, to Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - shi ne mafi kyauta ta alheri daga iskar da aka aiko.
عربي Turanci urdu
58. : : :
عربي Turanci urdu
59. "Shin kun san waye muflis (wanda aka yi wa wasoso)?* suka ce: Muflis a cikinmu wanda ba shi da dirhami ko kaya, sai ya ce: "Lallai cewa muflis daga al'ummata zai zo ranar alƙiyama da sallah da azumi da zakka, zai zo haƙiƙa ya zagi wannan, kuma ya yi wa wannan ƙazafi, ya ci dukiyar wannan, ya zubar da jinin wannan, ya daki wannan, sai a bawa wannan daga kyawawan ayyukansa, wannan ma daga kyawawan ayyukansa, idan kyawawan ayyukansa sun ƙare kafin a biya abin ke kansa sai a ɗauka daga kurakuransa sai a watsa masa, sannan a watsa shi a cikin wuta". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
60. ‘’Babu wani daga cikinku face sai Allah ya yi magana da shi, babu wani tafinta a tsakaninsu*, sai ya duba zuwa daman sa ba zai ga komai ba face abinda ya aikata, sai ya yi duba zuwa hagunsa shima ba zai ga komai ba face abinda ya aikata, sai ya yi duba zuwa gabansa ba zai ga komai ba sai wuta wajen fuskarsa, to ku ji tsoron wuta ko da kuwa da gutsiren dabino ne".
عربي Turanci urdu
61. Ya kai Ruwaifia,watakila rayuwarka tayi tsawo, saboda haka bawa Mutane labarin cewa duk wanda ya daure gemunsa, ko ya daura tsirkiya, ko yayi tsarki turoson dabbobi ko kashi, to babu shi babu Annabi Muhammad
عربي Turanci urdu
62. "Wanda ya zantar da wani Hadisi daga gareni yana ganin cewa shi ƙarya ne to shi yana ɗaya daga cikin maƙaryata". - 4 ملاحظة
عربي Turanci urdu
63. :
عربي Turanci urdu
64. : : : :
عربي Turanci urdu
65. Lallai cewa Manzon Allah SAW yayi Al-wala sai ya yi Alwala sai ya kuskure bakinsa, sannan ya face, sannan ya wanke fuskarsa sau Uku,da hannunsa na Dama sau Uku, xayanma sau uku, kuma ya shafi kansa da Ruwa ba na ragowar hannunsa ba, kuma ya wanke Qafarsa har ya tsaftace ta - 1 ملاحظة
عربي Turanci urdu
66. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana wanka, ko ya kasance yana wanka, da sa'i zuwa mudu biyar, kuma yana alwala da mudu.
عربي Turanci urdu
67. "Babu wani musulmin da zai yi alwala ya kyautata alwalarsa, sannan ya tashi ya yi sallah raka'a biyu, yana mai fuskantarsu da zuciyarsa da fuskarsa, sai aljanna ta wajaba gareshi"* Ya ce: Sai na ce: Ya mamakin kyan wannan, sai ga wani mai magana a gabana yana cewa: Wacce ke gabanta ta fi kyau, sai na duba sai ga Umar ya ce: Lallai ni na ganka ka zo ɗazu, ya ce: "Babu wani daga cikinku da zai yi alwala sai ya kai matuƙa - ko sai ya cika - alwalar sannan ya ce: Ina shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma (Annabi) Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne sai an buɗe masa kofofin aljanna takwas zai shiga ta wacce yake so". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
68. "Mala'iku ba sa shiga gidan da yake akwai kare ko hoto a cikinsa".
عربي Turanci urdu
69. "Kada ku yi rantsuwa da ɗagutai, ko da iyayenku".
عربي Turanci urdu
70. Duk wanda yayi alwala ranar juma'a zai samu lafiya, kuma duk wanda yayi alwala shine mafi alkhairi - 1 ملاحظة
عربي Turanci urdu
71. Idan ranar Juma'a mala'iku suka tsaya a kofar masallacin, sun rubuta na farko, sannan na farko
عربي Turanci urdu
72. "Kada ku zagi sahabbaina, da a ce ɗayanku zai ciyar da zinare kwatankwacin dutsen Uhudu ba zai kai cikin mudun ɗayansu ba, ko rabinsa".
عربي Turanci urdu
73. "Mafi alherin sahun maza shi ne na farkon su, kuma mafi sharrin su shi ne na ƙarshen su, mafi alherin sahun mata shi ne na ƙarshen su, kuma mafi sharrin su shi ne na farkon su".
عربي Turanci urdu
74. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi mana sallar Asuba wata rana sai ya ce: "Shin wane ya zo ne?" suka ce: A'a, ya ce: "Shin wane ya zo ne?" Suka ce: A'a, ya ce: @'Lallai waɗannan sallolin biyu sune mafi nauyin salloli akan munafuki, da kun san abinda ke cikinsu da kun zo musu koda da jan ciki ne akan gwiwowi*, kuma cewa sahun farko yana kan kwatankwacin sahun mala'iku, da ace kun san falalarsa da kun yi gaggawarsa. Lallai sallar namiji tare da namiji tafi tsarki daga sallarsa shi kaɗai, kuma sallarsa tare da maza biyu tafi tsarki daga sallarsa tare da namiji ɗaya, abinda ya yawaita to shine mafi soyuwa ga Allah - Maɗaukakin sarki -".
عربي Turanci urdu
75. "Lallai Allah Ya ƙetarewa al'ummata abinda ta yi tunanin shi a zuciya, muddin dai bata aikata ba ko ta yi magana ba".
عربي Turanci urdu
76. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce wa wata mata daga mutanen Madina, Ibnu Abbas ya ambaceta sai na manta sunanta: "Meya hanaki ki yi Hajji tare da mu?" Ta ce: Ba mu da komai sai raƙuma biyu, sai baban ɗanta da ɗanta suka yi Hajji akan raƙumi ɗaya, kuma ya bar mana ɗayan muna ban ruwa da shi, ya ce: @"Idan Ramadan ya zo to ki yi umara, domin umara a cikinsa yana daidai da Hajji". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu
77. : :
عربي Turanci urdu
78. "Na kasance tare da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya kai zuwa jujin wasu mutane, sai ya yi fitsari a tsaye,* sai na yi nesa, sai ya ce: "ka kusanto" sai na kusanto har na tsaya daura da maƙyangymansa sai ya yi alwala sai ya yi shafa akan kuffinsa biyu.
عربي Turanci urdu
79. "Kada ku yi hassada, kuma kada ku yi cinikin koɗe (shi ne wani ya zo sayan wani abu sai wani a kasuwar wanda ba ya nufin sayan sai ya zo ya ce a siyar mini a kaza sai ya faɗi sama da kuɗin kayan), kuma kada ku yi gaba, kada ku juyawa juna baya, kuma kada wani ya yi ciniki akan cinikin wani, ku zama bayin Allah 'yan uwan juna* Musulmi ɗan uwan musulmi ne, kada ya zalince shi kuma kada ya ƙi taimakonsa, kada ya wulaƙanta shi tsoron Allah a nan yake" - ya yi nuni zuwa ƙirjin sa, sau uku - "Ya ishi mutum sharri ya wulaƙanta ɗan uwansa musulmi, kowane musulmi akan musulmi haramun ne (ya zubda) jininsa, da dukiyarsa da mutuncinsa". Mutuncinsa". - 2 ملاحظة
عربي Turanci urdu