عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ أَنَّ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ قَالَ:

«مَنِ اغْتَسَلَ يَوْمَ الجُمُعَةِ غُسْلَ الجَنَابَةِ ثُمَّ رَاحَ، فَكَأَنَّمَا قَرَّبَ بَدَنَةً، وَمَنْ رَاحَ فِي السَّاعَةِ الثَّانِيَةِ، فَكَأَنَّمَا قَرَّبَ بَقَرَةً، وَمَنْ رَاحَ فِي السَّاعَةِ الثَّالِثَةِ، فَكَأَنَّمَا قَرَّبَ كَبْشًا أَقْرَنَ، وَمَنْ رَاحَ فِي السَّاعَةِ الرَّابِعَةِ، فَكَأَنَّمَا قَرَّبَ دَجَاجَةً، وَمَنْ رَاحَ فِي السَّاعَةِ الخَامِسَةِ، فَكَأَنَّمَا قَرَّبَ بَيْضَةً، فَإِذَا خَرَجَ الإِمَامُ حَضَرَتِ المَلاَئِكَةُ يَسْتَمِعُونَ الذِّكْرَ».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

An karbo daga Abi hurairata Allah ya kara yarda a gareshi- daga Annabi mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi- ya ce: {Duk wanda yayi wanka irin wankan janaba a ranar juma`ah, sa`annan ya tafi a farkon lokaci yana da ladan kamar ya bada sadakar babbar taguwa, wanda ya tafi a lokaci na biyu yana da ladan kamar ya bada sadakar saniya. wanda ya tafi a lokaci na uku yana da ladan kamar ya bada sadakar gajejen rago mai manyan kaho. wanda yatafi a lokaci na hudu yana da ladan kamar ya bada kaza. wanda kuma ya tafi a lokaci na biyar kamar ya bada kwan kaza. Idan liman ya fito sai mala`iku su halarto don sauraron Huduba}.
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Annabi yana bayyanawa cewa Falalar yin wanka da sammako zuwa Jumua, da kuma Darajar hakan, sai ya fadi cewa duk wanda yayi wanka Ranar Jumua kafin ya tafi Masallaci, sannan ya tafi a lokacin farko, to yana da ladan wanda ya bada sadakar Rakumin da ya yanka shi kuma ya bada naman sadaka, wanda kuma ya tafi a lokaci na biyu kamar wanda ya bada sadakar saniya ne, wanda kuma ya tafi a lokaci na uku, to kamar wanda ya bada sadakar Rago ne mai kaho guda biyu, kuma mafi yawa wannan yana kasancewa ne mafi kyawun Rago, kuma duk wanda ya tafi a lokaci na hudu kamar ya bada sadakar kaza, kuma duk wanda ya tafi a lokaci na biyar to kamar ya bada sadakar kwai ne, kuma idan Liman ya futo don Huduba da yin Sallah sai Mala'iku da ka wakilta da su Rubuta masu da jin Zikiri sai su tafi, duk wanda ya zo bayan sun tafi ba za'a Rubuta shi ba cikin makusantan Allah ba.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin

Ma"anonin Kalmomi