kase kashen kana nan rassa

lis din Hadisai

"An umarceni in yi sujjada akan gabbai bakwai*: Akan goshi sai ya yi nuni da hannunsa akan hancinsa, da hannaye, da gwiwoyi, da gefunan diga-digai, kuma kada ka tufke tufafi ko gashi".
عربي Turanci urdu
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana faɗa a tsakanin sujjada biyu; "Ya Ubangiji ka gafarta min, ka yi min rahama, ka ba ni lafiya, ka shiryar da ni, ka azurta ni.
عربي Turanci urdu
Cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana ɗaga hannayensa daura da kafaɗunsa in zai fara sallah,* haka nan in zai yi kabbara dan ruku'u, haka idan kuma zai ɗago kansa daga ruku'u sai ya ɗagasu, kuma ya ce: "Allah Ya ji wanda ya gode maSa, ya Ubangijinmu godiya ta tabbata gare ka, ya kasance ba ya yin haka a cikin sujjada.
عربي Turanci urdu
Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya sanar dani Tahiya, tafukana tsakanin tafukansa, kamar yadda yake sanar dani sura daga Alkur’ani *: "(Tsarkakan) Gaisuwa ta tabbata ga Allah, da salloli da tsarkake-tsarkake, aminci ya tabbata agareka Ya kai wannan Annabi da rahamar Allah da albarkarSa, aminci ya tabbata agaremu da bayin Allah na gari, ina shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma ina shaida cewa Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne". Acikin wani lafazi na su: "Lallai cewa Allah Shi ne aminci, idan dayanku ya zauna a cikin sallah to ya ce: (Tarakakan) Gaisuwa sun tabbata ga Allah da salloli da tsarkake-tsarkake, aminci ya tabbata agreka Ya kai wannan Annabi da rahamar Allah daalbarkarSa, aminci ya tabbata agaremu da bayin Allah na gari. Idan ya fadeta za ta samu kowanne bawan Allah nagari a sama da kasa, ina shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah ina shaida cewa Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzonsa ne, sannan ya zabi abin yake so ya roka".
عربي Turanci urdu
Ku daidaita a cikin sujjada, kar ku shimfida zira'oinku irin yadda kare ke shimfida nasa.
عربي Turanci urdu
Idan liman ya ce Ameen kuma ku ce Ameen ,domin duk wanda Ameen dinsa ta dace da ta Mala'iku to an gafarta masa abunda ya gabata na zunubansa.
عربي Turanci urdu
"Idan zaka yi sujjada, to ka sanya tafukanka ka kuma ɗaga gwiwowin hannunka".
عربي Turanci urdu
Idan Xayanku zai yi Sujada kada ya Durkusa kamar yadda Raqumi yake Durqusawa, ya fara sanya Hannayensakafin Guiwoyinsa
عربي Turanci urdu
Lallai cewa Ibn umar ya kasance yana sanya Hannayensa kafin guiwoyinsa, kuma ya ce: Manzon Allah SAW ya kasance yana yin hakan
عربي Turanci urdu
: . : .
عربي Turanci urdu
قل يأيها الكافرون قل هو الله أحد
عربي Turanci urdu
Lallai wasu mutane sun zo wa Sahlu ɗan Sa'ad Al-sa'idiy alhali sun yi musu a sha'anin minbarin (Manzon Allah) katakwayensa na mene ne, sai suka tambaye shi game da hakan, sai ya ce: Na rantse da Allah ni na san na mene ne su, haƙiƙa na gan shi a farkon ranar da aka ajiye shi, da kuma farkon ranar da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya fara zama a kansa, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya aika zuwa ga wance - wata mace daga Mutanen Madina -Sahlu ya ambace ta -; "Ki umarci yaronki kafinta ya haɗa min katakwaa da zan zauna a kansu idan zanyiwa mutane magana". Sai ta umarce shi sai ya yisu daga bishiyoyin daji, sannan ya zo da su, sai ta aika zuwa ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sai ya yi umarni aka ajiyesu a nan, sannan na ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi sallah a kansu ya yi kabbara alhali yana kansu, sannan ya yi ruku'u alahali yana kansu, sannan ya sauko da baya, sai ya yi sujjada a asalin minbarin sannan ya dawo, yayin da ya gama sai ya fuskanci mutane sai ya ce: "@ya ku mutane, kawai na aikata haka ne don ku yi koyi da ni, kuma ku san sallata".
عربي Turanci urdu
"Idan za ku yi sallah, to, ku daidaita sahunku, sannan ɗayanku ya yi muku limanci, idan ya yi kabbara sai ku yi kabbara*, idan ya ce: {Ba waɗanda ka yi fushi da su ba, ba kuma ɓatattu ba} [Al-Fatiha: 7], sai ku ce: Ameen, Allah zai amsa muku, idan ya yi kabbara ya yi ruku'u, sai ku yi kabbara ku yi ruku'u, domin cewa liman yana yin ruku'u ne kafinku, kuma yana ɗagowa ne kafinku", sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Waccan da waccan, idan ya ce: Allah Ya ji wanda ya gode maSa, sai ku ce: Ya Allah Ubangijinmu godiya ta tabbata gareKa, Allah Zai jiye muku (wato Zai amsa); domin cewa Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya faɗa a kan harshen AnnabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: Allah Ya ji wanda ya gode maSa, idan ya yi kabbara ya yi sujjada sai ku yi kabbara sai ku yi sujjada, domin cewa liman yana yin sujjada ne kafinku kuma yana ɗagowa ne kafinku", sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Waccan da waccan, idan an zo wurin zama; to, farkon abin da ɗayanku zai faɗa (shi ne): gaisuwa ta tabbata ga Allah tsarkakan salloli sun tabbata ga Allah, aminci ya tabbata a gareka ya kai wannan Annabi da rahamar Allah da albarkarSa, aminci ya tabbata a garemu da bayin Allah nagari, ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, ina shaida cewa (Annabi) muhammadu bawanSa ne, kuma manzonSa ne".
عربي Turanci urdu
Lallai ya kasance yana yin kabbara a kowacce sallar farilla da watanta, a Ramadan da waninsa, sai ya yi kabbara a yayin da yake miƙewa, sannan ya yi kabbara a yayin da yake yin ruku'u, sannan ya ce: Allah Ya ji wanda ya gode maSa, sannan ya ce: Ya Ubangijimmu godiya ta tabbata gareKa kafin ya yi sujjada, sannan ya ce: Allah ne mafi girma a yayin da yake tafiya ƙasa don yin sujjada, sannan ya yi kabbara a yayin da yake ɗago kansa daga sujjada, sannan ya yi kabbara a yayin da yake ɗago kansa daga sujjada, sannan ya yi kabbara a yayin da yake miƙewa daga zama a raka'a ta biyu, zai aikata haka a kowacce raka'a, har sai ya gama sallar, sannan ya ce a yayin da yake juyawa: @na rantse da wanda raina yake a hannunSa lallai ni ne mafi kusancinku kamanceceniya da sallar manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - wannan ita ce sallarsa har ya bar duniya.
عربي Turanci urdu
: :
عربي Turanci urdu
:
عربي Turanci urdu
Lallai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana faɗa a tsakanin sujjada biyu; "Ya Ubangijina Ka gafarta mini, ya Ubangijina Ka gafarta min'.
عربي Turanci urdu
Lallai ya zo wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - sai ya ce: Ya Manzon Allah, lallai haƙiƙa Shaiɗan ya shiga tsakanina da sallata da kuma karatuna, yana rikitar da ni, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "@Wannan wani Sahiɗan ne ana ce masa khinzab, idan ka ji shi ka nemi tsarin Allah daga gare shi, ka yi tofi a hagunka sau uku*", sai ya ce: Sai na aikata hakan sai Allah Ya tafiyar da shi daga gareni.
عربي Turanci urdu
Manzon Allah ya kasance in zaiyi salla sai yayi kabbara yayin da yake mikewa, sannan kuma yana yin kabbara yayin da yake yin ruku'u, sannan yana cewa: Allah ya ji mai gode masa, yayin da yake dago bayansa daga raka'a
عربي Turanci urdu
Na lura da sallar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- sai na sami tsayuwarsa, da ruku'unsa, da daidaitonsa bayan ruku'u,da sujjadarsa, da zamansa tsakanin sujjada biyu, da zamansa tsakanin sallama da juyawa: kusan daidai da daidai.
عربي Turanci urdu
Lallai cewa Annabi ya kasance yana Sallah kuma ya na dauke da Umama Yar Zainab Yar Annabi
عربي Turanci urdu
Na yi salla tare da Abu Bakr, Omar da Othman, kuma ban ji ɗayansu ya karanta "Da sunan Allah ba, Mai jin ƙai, Mai jin ƙai."
عربي Turanci urdu
Lallai cewa Annabi ya aika Wani Mutum a wani yaki sai ya kasane yana" karantawa abokansa in yana jansu Sallah, Sai yake cika karatunsa da: Kulhuwa.
عربي Turanci urdu
Ni da Imran bn Husayn mun yi salla a bayan Ali bin Abi Dalib, don haka idan ya yi sujjada, sai ya ce takbire, idan ya daga kansa sai ya ce takbire, idan kuma ya tashi daga rakaoin biyu, zai ce takbire.
عربي Turanci urdu
Na ji Annabi -tsira da amincin Allah- yana karanta Suratuddur a Sallar Magariba.
عربي Turanci urdu
Lallai ni wallahi zan yi muku sallah , amma ba sallar nake nufi ba, ina yin sallah ne yadda naga manzon Allah mai tsira da aminchi yake yin sallah.
عربي Turanci urdu
Naga Manzon Allah SAW yana yiwa Mutane limanci kuma umama Bint Abi Al-as ita ce Xiyar Zainab Xiyar Manzon Allah SAW tana kan kafaxarsa, idan yayi Ruku'u sai ya Ajiye ta, kuma idan ya Xago daga Sujada sai ya Mayar da ita
عربي Turanci urdu
Ku Kashe Baqaqe biyu ko a cikin Sallah ne: Macijiya da kuma Kunama
عربي Turanci urdu
Manzon Allah mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi ya kasance yana bude salla da yin kabbara, da karatu, da fadar Alhamdu lillahi rabbil aalamina, ya kasance idan yayi ruku`u baya dago kansa, baya kuma mikar da shi saidai tsaka tsaki
عربي Turanci urdu
Nayi Sallah tare da Manzon Allah SAW ya sanysa Hannunsa na Dama kan Hannunsa na Hagu akan Qirjinsa
عربي Turanci urdu
Abin da na yi a bayan wani kamar addu’ar Manzon Allah ne, amincin Allah ya tabbata a gare shi, daga haka-da-haka.
عربي Turanci urdu
Cewa Manzon Allah SAw ya kasance ian ya yayi Ruku'u yana rarraba 'Yanyatsunsa kuma idan yayi Sujada sai ya haxe su
عربي Turanci urdu
Lallai cewa Manzon Allah SAW idan ya kasanc a Wuturin Sallarsa baya tashi har sai ya daidaita a zaune
عربي Turanci urdu
Lallai cewa Manzon Allah SAW yayi Al-qunuti Wata xaya bayan Ruku'u yana Addu'a ga wasu Mutane daga Qabilar Bani Sulaim
عربي Turanci urdu
Lallai cewa Manzon Allah SAW ya kasance baya Al-qunuti sai in zai Addu'a ga wasu Mutane, ko yayi Addu'a kan wasu Mutane
عربي Turanci urdu
Ya Babana lallai kai kayi Sallah bayan Manzon Allah SAW da kuma Abubakar da Umar da Usman da Ali a nan Kufa, wajen Shekara Biyar, shin sun kasance suna Al-qunuti a Asuba? sai ya ce: Ai Xana Wannan fararre ne
عربي Turanci urdu
Manzon Allah SAW ya kasance idan ta zauna yana Addu'a, kuma yana sanya Hannunsa na dama akan cinyarsa ta dama kuma Hannunsa na Hagu kan cinyarsa ta Hagu, kuma yana nuni da Xanyatsansa na nuni, kuma yana sanya Babban Xanyatsansa a kan na tsakiya, kuma yana xora tafin Hannunsa na Hagu kan kan Guiwarsa
عربي Turanci urdu
Allah ka kuvutar da Ayyash Bn Abi rabi'a Ya Ubanhiji ka kuvutar da Sakamah Bn Hisham Ya Ubangiji ka kuvutar da Al-walid Bn Alwalid, Ya Ubangiji ka kuvutar da raunanan Muminai, Ya Ubangiji ka tsananta Kamunka ga Mudhar, Allah ka sanya musu yinwa kamar Shekarun Annabi Yusuf
عربي Turanci urdu
Manzon Allah mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi ya kasance yana bude salla da yin kabbara, da karatu, da fadar Alhamdu lillahi rabbil aalamina, ya kasance idan yayi ruku`u baya dago kansa, baya kuma mikar da shi saidai tsaka tsaki
عربي Turanci urdu
Cewa Manzon Allah SAW ya kasance idan zai kabbara yana xaga Hannayensa har sai sunkai daidai Kunnuwansa, kuma idan yayi ruku'u yana xaga Hannayensa har sukai daidai kunnuwansa
عربي Turanci urdu
Cewa Annabi-tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -ya shiga masallaci, sai wani mutum ya shigo, sai ya yi sallah, sannan (ya zo) ya yi sallama ga Annabi-tsira da amincin Allah su tabbata agare shi-sai ya amsa masa kuma ya ce: @Koma ka yi sallah domin cewa kai baka yi sallah ba"*, sai ya koma ya yi sallah kamar yadda ya yi sallar, sannan ya zo ya yi sallama ga-Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: "Koma ka yi sallah, domin cewa kai baka yi sallah ba" sau uku, sai ya ce: Na rantse da wanda ya aikoka da gaskiya ba zan iya yin wacce ta fita ba, to ka koya mini, sai ya ce: "Idan ka tashi zuwa sallah to ka yi kabbara, sannan ka karanta abinda ya sawwaka tare da kai na Alkur'ani, sannan ka yi ruku'u har sai ka natsu kana mai ruku'u, sannan ka dago har sai ka daidaita a tsaye, sannan ka yi sujjada har sai ka natsu kana mai sujjada, sannan ka dago har sai ka natsu a zaune, kuma ka aikata hakan acikin sallarka gaba dayanta".
عربي Turanci urdu