عن أبي هُرَيْرَةَ رضي الله عنه «أنَّ النبي صلى الله عليه وسلم دخل المسجد، فدخل رجل فصلَّى، ثم جاء فسلَّم على النبي صلى الله عليه وسلم فقال: ارجع فصلِّ، فإنك لم تُصَلِّ، فرجع فصلَّى كما صلَّى، ثم جاء فسلَّم على النبي -صلى الله عليه وسلَّم- فقال: ارجع فصلِّ، فإنك لم تُصَلِّ -ثلاثا- فقال: والذي بعثك بالحق لا أُحْسِنُ غيره، فَعَلِّمْنِي، فقال: إذا قُمْتَ إلى الصلاة فَكَبِّرْ، ثم اقرأ ما تيسر من القرآن، ثم اركع حتى تَطْمَئِنَّ راكعا، ثم ارفع حتى تعتدل قائما، ثم اسجد حتى تَطْمَئِنَّ ساجدا، ثم ارفع حتى تطمئن جالسا، وافعل ذلك في صلاتك كلها».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

An karbo daga Abi Huraira Allah ya yarda dashi"Cewa Annabi-tsira da amincin Allah su tabbata agareshi-ya shiga Masallaci,sai wani Mutum ya shigo yayi Salla,sannan yazo yayi sallama ga Annabi-tsira da amincin Allah su tabbata agareshi-sai yace:koma kayi Salla,domin cewa kai baka yi Salla ba.sai ya koma yayi Salla kamar yadda yayi Sallar,sannan yazo yayi sallama ga-Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agareshi- sai yace:koma kayi Salla,domin cewa kai bakayi Salla ba-sau Uku-sannan yace:Na rantse da wanda ya aikoka da Gaskiya bazan iya yin wacce tafita ba,to ka sanar dani,sai yace:Idan ka nufi yin Salla kayi Kabbara,sannan ka karanta abinda ya saukaka daga Al-Kur'ani,sannan kayi Ruku'u har sai ka daidaita kana mai Ruku'u,sannan ka dago har ka daidaita kana mai tsayuwa,sannan kayi Sajada har sai ka nutsu kana mai sajada,sannan ka dago har sai ka nutsu kana mai zama.kayi haka acikin kowace Sallarka.
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agareshi ya shiga Masallaci,sai wani Mutum daga cikin Sahabbai ya shigo,sunansa(Khallad Dan Rafi'u),sai yayi Salla gajeruwa ba cikakkun Aiyuka da karatuttuka,yayin da ya gama Sallarsa,sai yazo wajan Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agareshi, sai yayi masa Sallama sai Annabi ya mayar masa da sallama sannan yace dashi:koma kayi Salla,domin kai baka yi Salla ba.sai ya koma sai ya aikata ta biyun irin abinda yayi a Sallarsa ta Farkon,sannan yazo wajan Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agareshi, sai yace dashi:koma kayi Salla domin cewa kai baka yi Salla har sau Uku.sai Mutumin ya rantse da fadinsa:na rantse da wanda ya aikoka da gaskiya shine Allah Madaukaki bazan iya yin wacce tafi wacce nayi ba ka sanar dani.yayin da yayi kwadayin Ilimi,kuma Zuciyarsa ta soyu izuwa gareshi, yayi shirin karbarsa ya kore daukar kasantuwarsa mai Mantuwa bayan tsawaon kokkomawarsa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace dashi abinda ma'anarsa:idan ka tsaya yin Salla to kayi kabbara kabbarar Harama,sannan ka karanta abinda ya sauwaka daga Al-Kur'ani, bayan karanta Fatiha sannan kayi Ruku'u har sai ka nutsu kana mai Ruku'u, sannan ka dago daga Ruku'u har sai ka daidaita a tsaye, kuma ka nutsu a daidaiton naka sannan kayi sajada har sai ka nutsu kana mai sajada,a

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin