عن حُذَيْفَةَ رضي الله عنه:
أَنَّ النَّبِيَّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ كَانَ يَقُولُ بَيْنَ السَّجْدَتَيْنِ: «رَبِّ اغْفِرْ لِي، رَبِّ اغْفِرْ لِي».

[صحيح] - [رواه أبو داود والنسائي وابن ماجه وأحمد] - [سنن ابن ماجه: 897]
المزيــد ...

Daga Huzaifa - Allah Ya yarda da shi -:
Lallai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana faɗa a tsakanin sujjada biyu; "Ya Ubangijina Ka gafarta mini, ya Ubangijina Ka gafarta min'.

[Ingantacce ne] - [Abu Daud da Nasa'i da Ibnu Majah da Ahmad ne suka Rawaito shi] - [Sunanu Ibn Majah - 897]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana faɗa a yayin zama a tsakaknin sujjada biyu: Ya Ubangina ka gafarta min, yana maimaita ta.
Ma'anar ya Ubangijina Ka gafarta min: Bawa yana neman daga Ubangijinsa ya shafe masa zunubansa ya suturta aibukansa.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Shar’antuwar wannan addu'ar a tsakanin sujjada biyu a sallar farilla da nafila.
  2. An so maimaita faɗin: Ya Ubangijina Ka gafarta min, wajibi (shi ne) sau ɗaya.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (58)