عَنْ طَاوُسٍ أَنَّهُ قَالَ: أَدْرَكْتُ نَاسًا مِنْ أَصْحَابِ رَسُولِ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ، يَقُولُونَ كُلُّ شَيْءٍ بِقَدَرٍ، قَالَ: وَسَمِعْتُ عَبْدَ اللهِ بْنَ عُمَرَ رضي الله عنهما يَقُولُ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«كُلُّ شَيْءٍ بِقَدَرٍ، حَتَّى الْعَجْزِ وَالْكَيْسِ، أَوِ الْكَيْسِ وَالْعَجْزِ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 2655]
المزيــد ...

Daga Dawus cewa shi ya ce: Na riski wasu mutane daga sahabban Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suna cewa kowane abu (yana kasancewa) da kaddara ne, ya ce: Na ji Abdullahi Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su, yana cewa: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce:
"Kowanne abu da kaddara ne, har gajiya da dabara, ko kuma wayo da gajiya ".

[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [Sahih Muslim - 2655]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa kowanne abu da kaddara ne; Har kasawa: ita ce: Barin abinda yake wajibi ne aikata shi, da cewa zai yi ta jinkirta shi daga lokacinsa, da al'amuran duniya da lahira. Har dabara ita ce: Nishadi da kwarewa da al'amuran duniya da lahira. Kuma cewa Allah - Mai girma da daukaka - hakika Ya kaddara gajiyawa da wayo da kowane abu, ba zai afku a kasantacce ba sai hakika sanin Allah Ya rigaya da shi da mashi'arSa.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Bayanin kudircewar sahabbai - Allah Ya yarda da su - a kaddara.
  2. Kowanne abu yana faruwa ne da kaddarawar Allah har gajiyawa da kuma nishadi.
  3. Ya tabbata kuma sahabbai - Allah Ya yarda da su, sun tsoratar - a cikin riwayar hadisan Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
  4. Yin imani da kaddara dukkaninsa alherinSa da kuma sharrinSa.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (65)