عن عبد الله بن عباس رضي الله عنهما قال: كنت خلف النبي صلى الله عليه وسلم يوماً فقال يا غلام، إني أعلمك كلمات: «احْفَظِ اللهَ يحفظْك، احفظ الله تَجِدْه تُجَاهَك، إذا سألت فاسأل الله، وإذا اسْتَعَنْتَ فاسْتَعِن بالله، واعلمْ أن الأمةَ لو اجتمعت على أن ينفعوك بشيء لم ينفعوك إلا بشيء قد كتبه الله لك، وإن اجتمعوا على أن يَضرُّوك بشيء لم يَضرُّوك إلا بشيء قد كتبه الله عليك، رفعت الأقلام وجفت الصحف». وفي رواية: «احفظ الله تَجِدْه أمامك، تَعرَّفْ إلى الله في الرَّخَاء يَعرِفْكَ في الشِّدة، واعلم أنَّ ما أخطأَكَ لم يَكُنْ ليُصِيبَكَ، وما أصَابَكَ لم يَكُنْ لِيُخْطِئَكَ، واعلم أن النصرَ مع الصبرِ، وأن الفرجَ مع الكَرْبِ، وأن مع العُسْرِ يُسْرًا».
[صحيح] - [رواه الترمذي وأحمد بروايتيه]
المزيــد ...

Daga Abdullahi Dan Abbas zuwa ga Annabi "Ka kiyaye, Allah sai Allah ya kiyaye ka, ka kiyaye Allah Sai ka same shi duk halin da kasamu kanka, kuma idan zaka roki wani abu to ka roki Allah, kuma idan zaka nemi taimako to ka nemi taimakon Allah kuma kasani cewa da Al'umma zasu taru kan su amfanar da kai wani abu bazasu iya amfanar da kai da komai sai dai da abinda Allah ya rubuta maka shi, kuma da ace zasu taru da niyyar su cutar da kai to bazasu iya cutar dakai da komai ba sai da abinda Allah ya rubuta maka, kuma a dage Alkalami kuma takardun sun bushe, a wata riwayar kuma: "Ka kiyaye Allah Sai ka same shi a duk inda ka dosa, kuma ka tuna Allah lokacin kake cikin wadata sai ya tuna da kai lokacin da ka shiga tsanani, kuma kasani cewa duk abinda ya kuskureka daman cewa to ba'a rubuta zai sameka ba, kuma duk abinda ya sameka daman can rubuta zai same ka, kuma cewa lallai Nasara tana tare da Mai hakuri, kuma yayewar bakin ciki na tare da mai bakin cikin, kuma lallai cewa sauki na tafe bayan tsanani"
Ingantacce ne - Al-Tirmithi Ya Rawaito shi

Bayani

Cikin wannan Hadisin Mai girma kuma Annabi yana koyar da wannan Yaro kuma yaron shi ne Dan Abbas da wasiyyoyi manya wacce ta kunshi cewa ya kiyaye umarnin Allah kuma ya kiyaye haninsa a kowane lokutansa, kuma Annabi ya gyara masa Akidarsa tun yana Yaro cewa babu wani mahallici sai Allah, kuma babu wani mai iko sama da Allah, kuma babu wani mai gudanar da rayuwar mutane tare da Allah, kuma cewa babu wani tsani tsakanin bawa da Ubangijinsa, to Allah shi ne abin dogara lokacin saukar Bala'i, kuma Allah shi ne abin kauna lokacin faruwar ukuba, kuma Annabi ya dasa a zuciyar Dan Abbas -Allah ya yarda da shi- Imani da Kaddarar Allah da kuma kaddararsa to dukkan komai da kaddararsa ne da kuma Hukuncinsa.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Jamusanci Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin