Karkasawa: Aqida .

عن أبي ذر الغفاري رضي الله عنه عن النبي صلى الله عليه وسلم فيما يرويه عن ربه: «يا عبادي، إني حرَّمتُ الظلمَ على نفسي وجعلتُه بينكم محرَّمًا فلا تَظَالموا، يا عبادي، كلكم ضالٌّ إلا من هديتُه فاستهدوني أَهْدَكِم، يا عبادي، كلكم جائِعٌ إلا من أطعمته فاستطعموني أطعمكم، يا عبادي، كلكم عارٍ إلا من كسوتُه فاسْتَكْسُوني أَكْسُكُم، يا عبادي، إنكم تُخطئون بالليل والنهار وأنا أغفر الذنوبَ جميعًا فاستغفروني أغفرْ لكم، ياعبادي، إنكم لن تَبلغوا ضَرِّي فتَضُرُّونِي ولن تَبْلُغوا نَفْعِي فتَنْفَعُوني، يا عبادي، لو أن أولَكم وآخِرَكم وإنسَكم وجِنَّكم كانوا على أتْقَى قلبِ رجلٍ واحد منكم ما زاد ذلك في ملكي شيئًا، يا عبادي، لو أن أوَّلَكم وآخِرَكم وإنسَكم وجِنَّكم كانوا على أفْجَرِ قلب رجل واحد منكم ما نقص ذلك من ملكي شيئًا، يا عبادي، لو أن أولكم وآخركم وإنسكم وجنكم قاموا في صَعِيدٍ واحد فسألوني فأعطيت كلَّ واحدٍ مسألتَه ما نقص ذلك مما عندي إلا كما يَنْقُصُ المِخْيَطُ إذا أُدخل البحر، يا عبادي، إنما هي أعمالكم أُحْصِيها لكم ثم أُوَفِّيكُم إياها فمن وجد خيرًا فليحمد الله ومن وجد غير ذلك فلا يلومن إلا نفسه».
[صحيح] - [رواه مسلم]
المزيــد ...

Daga Abu Thar Al'ghifari -ALlah ya yarda da shi daga Annabi- cikin abi nda ya rawaito shi daga Ubangijinsa Mai girma da Daukaka: "Yaku Bayi na Lallai ni na Haramta zalunci a kankin kaina kuma na sanya shi ya zama haramtacce a tsakanin to kada kuyi Zalunci, ya ku Bayi na dukkanninku Batattu ne sai wanda na shiryar to ku nemi shiriya ta, sai na shiryar da ku ya ku Bayina Dukkanninku Mayinwata ne sai wanda na na viyar da shi to kunemi ciyarwa ta sai inciyar daku, Ya ku Bayina Dukkanninku Funtaye ne sai wanda na tufatar da shi to ku nemi tufatarwa ta sai in tufatar da ku, ya ku Bayina cewa ku kuna yin laifuffuka dare da rana ni kuma ina gafarta zunu bai baki daya daya ko nemi gafara ta sai in gafarta muku, ya ku bayina baku isa ku iya cutar dani ba ballanta ku cutar kuma baku isa ku iya amfanar da ni ba ballantana ku amfanar dani ballantana ku amfanar da ni, kuma da ace na farkonku da na karshenku da Muatanenku da Aljanunku zasu zamanto kamar zuciyar daya Mafi tsoron Allah daga cikinku wannan ba zai kari Mulki na da komai ba kuma da ace na farkonku da na karshenku da Muatanenku da Aljanunku zasu zamanto kamar zuciyar daya Mafi fajirci daga cikinku wannan ba zai rage Mulki na da komai ba ya ku Bayina da ace na farkonku da na karshenku da Mutanenku da Aljanunku zasu taru a bigire kwaya daya kuma kowanne ya fadi bukatarsa kuma na biyawa kowa bukatarsa hakan ba zai tauye komai ba na daga abunda yake wurina in ma zai rage sai dai in kamar a saka Allura a cikin Kogi, Ya ku Bayina Wannan dai ayyukanku ne nake kiyaye muku su kuma sannan in saka muku da su to duk wanda ya samu Alkairi to ya godewa Allah kuma duk wanda ya samu wanin hakan to kada ya zargi kowa sai kansa"
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

Wannan Hadisin Kudusi yana koyar da mu abubuwa a cikin Ginshikan addini, da kuma rassan sa,da kuma ladaban sa , cewa lallai Allah Mai girma da Daukaka ya Haramta Zalunci akankin kansa don falalarsa da kuma kyautatawarsa ga bayinsa, kuma ya sanya Zalunci Haramtacce a tsakaninku kada dayanku ya kuskura yayi zalunci, kuma cewa lallai bayi duka batattu ne sai wanda Allah ya shiryar da shi da shiriyar sa da kuma datarwar sa, kuma duk wanda ya roki Allah Allah zai shiyar da shi kuma ya datar da shi , kuma cewa Bayinsa Mabukata ne izuwa gare shi, kuma duk wanda ya roke shi zai biya masa bukatunsa kuma zai isar masa, kuma cewa su suna yin zunubai dare da rana kuma Allah yana suturta su kuma yana kau da kai duk lokacin da Bawa ya nemi gafara,kuma bazasu taba iyawa ba ko sun yi kokarin yi da maganar su ko aikinsu su cutar da Allah ko su amfanar da shi, kuma da ace zasu zamanto dai dai da zuciyar mafi tsoron Allah daga cikinsu ko mafi fajircin daya daga cikinsu don su amafanar da Allah ko su cutar da shi bazasu iya tauye komai ba a cikin Mulkinsa, domin su raunana ne kuma Mabukata izuwa gare shi a kowane lokaci da kuma zamani da kuma ko ina suke, kuma da ace zasu taru a bigire daya kuma su roki Allah zai biyawa kowa bukatarsa ba tare da wani daga abinda yake gurin Allah ba; domin taskokinsa cike suke ciyarwa bata karar da ita, komai dare komai rana, kuma Allah yana kiyaye musu dukkan Ayyukan bayi abunda suka aikata da abinda aka nema su aikata, sannan ya biya su ladansa a ranar Alkiyama to duk wanda ya sami sakamakon aikin Alkairi ya godewa Allah da ya datar da shi da aikin Alheri, kuma duk wanda ya samu wanin haka to kada ya zargi kowa sai kansa da zuciyarsa mai umarni da Mummunan aiki wacce ta jashi zuwa Asara.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Jamusanci Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin