عن أبي موسى الأشعري رضي الله عنه مرفوعاً: «إن الله ليُمْلِي للظالم، فإذا أخذه لم يُفْلِتْهُ»، ثم قرأ: (وكذلك أخذ ربك إذا أخذ القرى وهي ظالمة إن أخذه أليم شديد).
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...
An rawaito daga Abu Musa Al-ash'ari -Allah ya yarda da shi- daga Annabi: "Lallai Alla Madaukakin Sarki yana talala ga Azzalumi, idan ya kama shi ba zai kwace masa ba" sannan ya karanta: (Kuma haka Ubangijinka yake kamu idan ya kama Al-karyu a halin suna Zaluntar kawunan su" lallai Kamunsa Mai radadi ne kuma mai tsanani)
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]
Tsira da Amincin ALlah su tabbata a gae shi yana bamu labarin cewa Allah mai girama da daukaka yana yin talala ga Azzalumi kuma yana kyale shi yana zaluntar kansa; har sai ya kama shi ba zai kyale shi ba, har sai ya cika masa ukubarsa, sannan ya karanta -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-fadin Allah Madaukakin sarki: "Haka Ubangijinka yake kamu idan yakama Mutanen Alkaryu a halin suna Zaluntar kawunansu, lallai kamunsa Mai radadi ne kuma Mai tsanani"