Karkasawa: Aqida .

عن أبي موسى الأشعري رضي الله عنه مرفوعاً: «إن الله ليُمْلِي للظالم، فإذا أخذه لم يُفْلِتْهُ»، ثم قرأ: (وكذلك أخذ ربك إذا أخذ القرى وهي ظالمة إن أخذه أليم شديد).
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Wannan fassarar tana bukatar Karin bita da gyaran yare.

An rawaito daga Abu Musa Al-ash'ari -Allah ya yarda da shi- daga Annabi: "Lallai Alla Madaukakin Sarki yana talala ga Azzalumi, idan ya kama shi ba zai kwace masa ba" sannan ya karanta: (Kuma haka Ubangijinka yake kamu idan ya kama Al-karyu a halin suna Zaluntar kawunan su" lallai Kamunsa Mai radadi ne kuma mai tsanani)
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Tsira da Amincin ALlah su tabbata a gae shi yana bamu labarin cewa Allah mai girama da daukaka yana yin talala ga Azzalumi kuma yana kyale shi yana zaluntar kansa; har sai ya kama shi ba zai kyale shi ba, har sai ya cika masa ukubarsa, sannan ya karanta -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-fadin Allah Madaukakin sarki: "Haka Ubangijinka yake kamu idan yakama Mutanen Alkaryu a halin suna Zaluntar kawunansu, lallai kamunsa Mai radadi ne kuma Mai tsanani"

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Jamusanci Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية
Manufofin Fassarorin