عَنْ مَطَرِ بْنِ عُكَامِسٍ رضي الله عنه قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«إِذَا قَضَى اللَّهُ لِعَبْدٍ أَنْ يَمُوتَ بِأَرْضٍ جَعَلَ لَهُ إِلَيْهَا حَاجَةً».

[صحيح] - [رواه الترمذي]
المزيــد ...

Daga Madar Dan Ukamis - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:
"Idan Allah Ya kaddarawa bawa cewa zai mutu a wata kasa sai Ya sanya masa wata bukata zuwa gareta".

Ingantacce ne - Al-Tirmithi Ya Rawaito shi

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bada labarin cewa Allah idan Ya hukunta Ya kuma kaddarawa bawa cewa zai mutu a wata kasa alhali shi ba ya cikin kasar; sai a sanya masa wata bukata gareta sai ya tafi kasar, sai a karbi ransa a cikinta.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Hadisin gasgatawa ne ga fadin Allah - Mai girma da daukaka -: {Kuma wata rai ba ta sanin a wacce kasa zata mutu}.