عن أبي هريرة رضي الله عنه عن رسول الله صلى الله عليه وسلم قال: "كَلِمَتَانِ خفيفتان على اللسان، ثقيلتان في الميزان، حبيبتان إلى الرحمن: سبحان الله وبحمده، سبحان الله العظيم".
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...
An karbo daga Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- daga Manzon Allah -tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: "Kalmomi Biyu Masu Soyiwa a wajen Allah, kuma Masu saukin fada a Harshe, kuma masu Nauyi a Ma'auni, Tsarki ya tabbata ga Allah da kuma godiya gare shi, Tsarki ya tabbata ga Allah Maigirma"
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]
Annabi ya bada Labari a cikin wanna Hadisin cewa Ubangiji mai Rahama yana son wandan nan Kalmomi biyu Masu karancin Harafai ga su da Nauyin Ma'auni, Tsarki ya tabbata ga Allah da godiya a gare shi, tsarki ya tabbata ga Allah Mai girma; saboda abunda suka kunsa na tsarkake Allah da kuma Tasbihi a gare shi daga dukkan Tawaya daga kuma duk abun da bai dace da daukakarsa ba, da kuma Karfafawa kan Wannan tsarkakewar da Sifanta shi da Girma.