عن أبي هريرة رضي الله عنه أن رسول الله صلى الله عليه وسلم قال:
«حُجِبَتِ النَّارُ بِالشَّهَوَاتِ، وَحُجِبَتِ الْجَنَّةُ بِالْمَكَارِهِ».

[صحيح] - [رواه البخاري] - [صحيح البخاري: 6487]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira Allah - Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce:
"An kewaye wuta da sha'awowi, kuma an kewaye Aljanna da abubuwa ki".

[Ingantacce ne] - [Bukhari ne ya rawaito shi] - [Sahih Al-Bukhari - 6487]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bayyana cewa wuta abar kewayewace da al'amuran da rai take son sha'awrsu na aikata abubuwan da aka haramta, ko takaitawa a wajibai; Duk wanda ya bi son ransa a hakan to ya cancanci wuta, Kuma cewa Aljanna abar kewayewace da al'amuran da rai take kin su; kamar lazimta akan abubuwan da aka umarta da barin abubuwan da aka haramta, da hakuri akan hakan, idan ya kutsa kuma ya yaki ransa a hakan to ya cancanci shiga Aljanna.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Daga sabubban afkawa a sha'awowi kawatawar Shaidan abin ki da mummuna, har rai ya gan shi mai kyau ne, sai ya karkata zuwa gare shi.
  2. Umarni da nisantar sha'awowin da aka haramta; domin cewa su hanya ce zuwa wuta, da kuma hakuri akan abubuwan ki; domin cewa su hanya ce ta zuwa Aljanna.
  3. Falalar yakar rai ko kokari a ibada, da kuma hakuri akan abubuwan ki da wahalar da ke kewaye ayyukan biyayya.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (67)