عَنْ حَكِيمِ بْنِ حِزَامٍ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ قَالَ:
سَأَلْتُ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ فَأَعْطَانِي، ثُمَّ سَأَلْتُهُ فَأَعْطَانِي، ثُمَّ قَالَ لِي: «يَا حَكِيمُ، إِنَّ هَذَا المَالَ خَضِرٌ حُلْوٌ، فَمَنْ أَخَذَهُ بِسَخَاوَةِ نَفْسٍ، بُورِكَ لَهُ فِيهِ، وَمَنْ أَخَذَهُ بِإِشْرَافِ نَفْسٍ لَمْ يُبَارَكْ لَهُ فِيهِ، وَكَانَ كَالَّذِي يَأْكُلُ وَلاَ يَشْبَعُ، وَاليَدُ العُلْيَا خَيْرٌ مِنَ اليَدِ السُّفْلَى»، قَالَ حَكِيمٌ: فَقُلْتُ: يَا رَسُولَ اللَّهِ، وَالَّذِي بَعَثَكَ بِالحَقِّ لاَ أَرْزَأُ أَحَدًا بَعْدَكَ شَيْئًا حَتَّى أُفَارِقَ الدُّنْيَا، فَكَانَ أَبُو بَكْرٍ يَدْعُو حَكِيمًا لِيُعْطِيَهُ العَطَاءَ، فَيَأْبَى أَنْ يَقْبَلَ مِنْهُ شَيْئًا، ثُمَّ إِنَّ عُمَرَ دَعَاهُ لِيُعْطِيَهُ، فَيَأْبَى أَنْ يَقْبَلَهُ، فَقَالَ: يَا مَعْشَرَ المُسْلِمِينَ، إِنِّي أَعْرِضُ عَلَيْهِ حَقَّهُ الَّذِي قَسَمَ اللَّهُ لَهُ مِنْ هَذَا الفَيْءِ، فَيَأْبَى أَنْ يَأْخُذَهُ. فَلَمْ يَرْزَأْ حَكِيمٌ أَحَدًا مِنَ النَّاسِ بَعْدَ النَّبِيِّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ حَتَّى تُوُفِّيَ رَحِمَهُ اللَّهُ.
[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 2750]
المزيــد ...
Daga Hakim ɗan Hizam - Allah Ya yarda da shi - ya ce::
Na roki Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya bani, sannan na sake rokonsa sai ya bani, sannan ya ce da ni: «Ya Hakim lallai ita wannan dukiyar koriya ce mai zaƙi, wanda ya karɓeta da wadatar rai, za’a yi masa albarka a cikinta, wanda ya karɓeta da ɗaukakar rai ba za’a yi masa albarka a cikinta ba, sai ya zama kamar wanda yake ci ne ba ya ƙoshi, hannu maɗaukaki shi ne mafi alheri daga hannu maƙasƙanci». Hakim ya ce: Sai na ce: Ya Manzon Allah, na rantse da wanda ya aikoka da gaskiya ba zan taɓa tauye wa wani, wani abu ba a bayanka har na bar duniya, Abubakar ya kasance yana kiran Hakim dan ya bashi kyauta (daga Baitul mali), sai ya ƙi karɓar komai daga gurinsa, sannan Umar ya kira shi dan ya ba shi, sai ya ƙi karɓa, sai ya ce: Yaku jama'a musulmai, lallai cewa ni ina ba shi haƙƙinsa wanda Allah Ya raba masa daga wannan ganimar, sai ya ƙi karɓarsa, Hakim bai tauyewa wani mutum daga cikin mutane ba bayan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ba - har sai da ya rasu - Allah ya yi masa rahama -.
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح البخاري - 2750]
Hakim ɗan Hizam - Allah Ya yarda da shi - ya tambayi Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - wani abu na jin daɗin duniya sai ya ba shi, sannan ya roke shi karo na biyu sai ya ba shi, sannan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce masa: Ya Hakim, lallai cewa wannan dukiyar abar sha'awace abar so ce, wanda ya sameta ba tare da roƙo ba kuma ya karɓeta ba tare da zari da kuma naci ba, za’a yi masa albarka a cikinta, wanda ya karɓeta da tsinkayar rai da kuma kwaɗayi ba za’a yi masa albarka a cikinta ba, zai zama kamar wanda yake ci ba ya ƙoshi, hannu maɗaukaki mai bayarwa shi ne mafi alheri a wurin Allah daga hannu maƙasƙanci mai roƙo. Hakim ya ce: Sai na ce: Ya Manzon Allah, na rantse da wanda Ya aikoka da gaskiya ba zan karbi dukiyar wani ba ta hanyar roko daga gare shi ba a bayanka har na bar duniya. Halifan Manzon Allah Abubakar - Allah Ya yarda da shi - ya kasance yana kiran Hakim dan ya ba shi rabonsa daga baitul mali, sai ya ƙi karɓar komai daga gare shi, sannan sarkin muminai - Umar - Allah Ya yarda da shi - ya kira shi dan ya ba shi ita, sai ya ƙi karɓarta, sai Umar ya ce: Yaku taron jama'ar musulmai, lallai ni ina ba shi haƙƙinsa wanda Allah Ya raba masa daga ganimar da musulmai suka samu daga kafirai ba tare da ya ƙi ba, sai ya ƙi karɓarta, bayan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - Hakim bai rage dukiyar kowa ba ta hanyar nemanta har ya yi wafati - Allah Ya yarda da shi -.