+ -

عن جابر بن عبد الله رضي الله عنهما قال: سمعت رسول الله صلى الله عليه وسلم يقول:
«مَنْ لَقِيَ اللهَ لَا يُشْرِكُ بِهِ شَيْئًا دَخَلَ الْجَنَّةَ، وَمَنْ لَقِيَهُ يُشْرِكُ بِهِ دَخَلَ النَّارَ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 93]
المزيــد ...

Daga Jabir Dan Abdullahi - Allah Ya yarda da su - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa:
"Wanda ya gamu da Allah ba ya tarayya da shi da wani to zai shiga Aljanna, wanda kuma ya gamu da shi yana shirka da shi to zai shiga wuta".

[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 93]

Bayani

Annabi - tsiara da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana sanar da cewa wanda ya mutu ba ya hada Allah da kowa to makaomarsa ita ce Aljanna , koda an azabtar da shi akan sashin zunubansa, kuma cewa wanda ya mutu alhali shi yana tarayya da Allah to zai dawwama a wuta.

Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Jamusanci Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية Kirgisisch النيبالية Yoruba الليتوانية الدرية الصومالية الطاجيكية Kinyarwanda الرومانية المجرية التشيكية Malagasy Italiyanci Oromo Kanadische Übersetzung Aserbaidschanisch الأوزبكية الأوكرانية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Falalar Tauhidi, kuma cewa shi sababi ne na tsira daga dawwama a wuta.
  2. Kusancin Aljanna da wuta ga bawa, kuma cewa shi babu wani abu a tsakaninsa da su sai mutuwa.
  3. Gargadi daga shirka, kadan dinta da mai yawanta; domin cewa tsira daga wuta ta hanyar nisantar ta ne.
  4. Izina a ayyuka da karshen su ne.