عن جابر بن عبد الله رضي الله عنهما قال: سمعت رسول الله صلى الله عليه وسلم يقول:
«مَنْ لَقِيَ اللهَ لَا يُشْرِكُ بِهِ شَيْئًا دَخَلَ الْجَنَّةَ، وَمَنْ لَقِيَهُ يُشْرِكُ بِهِ دَخَلَ النَّارَ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 93]
المزيــد ...

Daga Jabir Dan Abdullahi - Allah Ya yarda da su - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa:
"Wanda ya gamu da Allah ba ya tarayya da shi da wani to zai shiga Aljanna, wanda kuma ya gamu da shi yana shirka da shi to zai shiga wuta".

[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [Sahih Muslim - 93]

Bayani

Annabi - tsiara da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana sanar da cewa wanda ya mutu ba ya hada Allah da kowa to makaomarsa ita ce Aljanna , koda an azabtar da shi akan sashin zunubansa, kuma cewa wanda ya mutu alhali shi yana tarayya da Allah to zai dawwama a wuta.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Falalar Tauhidi, kuma cewa shi sababi ne na tsira daga dawwama a wuta.
  2. Kusancin Aljanna da wuta ga bawa, kuma cewa shi babu wani abu a tsakaninsa da su sai mutuwa.
  3. Gargadi daga shirka, kadan dinta da mai yawanta; domin cewa tsira daga wuta ta hanyar nisantar ta ne.
  4. Izina a ayyuka da karshen su ne.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (67)