عن أبي هريرة رضي الله عنه قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم : «لا تجعلوا بيوتكم قبورا، ولا تجعلوا قبري عيدا، وصلوا عليّ فإن صلاتكم تبلغني حيث كنتم».
[صحيح] - [رواه أبو داود]
المزيــد ...
Daga Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- Zuwa ga Annabi: "ada ku Sanya gidajenku Kabari, kima kada ku sanya Kabari na wajen Biki, kuyi Salati domin duk inda kuke zai same ni,
[Ingantacce ne] - [Abu Daud Ya Rawaito shi]
Annabi ya hana wofuntar da dakuna daga Nafilfili a cikinsu, da kuma Addua da Karatun Alqurani to sai su zamanto kamar Kaburbur; domin hani da barin yin Sallah a kaburbura ya tabbata a garesu to sai ya hanasu su sanya gidajensu su zamanto kaburbura suma, kuma ya hana maimaita ziyarar kabarinsa da taruwa a gurinsa ta hanayar Al'ada; domin hakan hanaya ce izuwa shirka, kuma yayi Umarni da wadatuwa da yawaita yin Salati a gare shi a ko'ina kuke a bayan kasa; domin hakan cewa yana uwan masa daga kusa ne ko daga nesa ne don haka babu wata bukatar kaikomon zuwa Kabarinsa.