عن طارق بن أشيم الأشجعي مرفوعاً: "من قال لا إله إلا الله، وكَفَرَ بما يُعْبَدُ من دون الله حَرُمَ مالُه ودمُه وحِسابُه على الله".
[صحيح] - [رواه مسلم]
المزيــد ...
Daga Dariq Bn Ashyam Al-ashja'i daga Manzon Allah "Duk wanda ya fadi "La'ilaha illAllah", kuma ya kafircewa duk wani abin da ake bautawa ba Allah ba, an haramta taba dukiyarsa da jininsa,kuma sakamakonsa yana ga Allah Madaukaki".
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi
Manzon Allah SAW yana bayani a wannan Hadisin cewa shi bai haramta kashe Mutum ko kwace dukiyarsa ba sai in abubuwa biyu sun tattaru akansa: Na daya: Fadin Babu Wani Ubangiji sai Allah -Madaukaki- Na biyu: Kafircewa da da bautar abunda ake bautawa wanin Allah Madaukakin Sarki, saboda idan aka samu rashin Wadan nan abubuwan guda biyu, ya wajaba a kame ga barin tabashi a fili da kuma barin komai nasa ga Allah _Madaukakin Sarki- Matukar dai baizo da abunda zai halartar da Jininsa ba Kamar Ridda, ko Dukiyarsa, Kmar kin bada Zakka ko kuma Mutuncinsa Kamar Taurin kin biyan bashi