عن عبد الله بن مسعود قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم:
«هلك المُتَنَطِّعُون» قالها ثلاثًا.
[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 2670]
المزيــد ...
Daga Abdullahi Dan Mas'ud ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce:
"Masu tsanantawa sun halaka" ya fadi hakan ne har sau uku.
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana bada labari game da tabewar masu tsanantawa - ba tare da shiriya da ilimi ba - a addinin su da duniyar su, da kuma maganganun su da ayyuakan su, masu ketare iyakar shari'a da su wanda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zo da shi.