عن ابن عباس رضي الله عنهما في قول الله تعالى : (وَقَالُوا لا تَذَرُنَّ آلِهَتَكُمْ وَلا تَذَرُنَّ وَدًّا وَلا سُوَاعًا وَلا يَغُوثَ وَيَعُوقَ وَنَسْرًا) قال: "هذه أسماء رجال صالحين من قوم نوح، فلما هَلَكوا أَوحى الشَّيطان إلى قَومِهِم أنِ انْصِبُوا إلى مَجَالِسِهِم الَّتي كانوا يَجْلِسون فيها أنصَابًا، وسَمُّوها بأسمَائِهِم، فَفَعَلُوا، ولم تُعْبَد، حتَّى إِذَا هَلَك أُولئك ونُسِيَ العلم عُبِدت".
[صحيح] - [رواه البخاري]
المزيــد ...

Daga Dan Abbass cikin fadin Allah inda yake cewa: kuma suka ce kada ku kuskura ku bar Allolinku kuma kada ku bar Waddan da Suwa'an da kuma Yagusa da ya'uka da kuma Nasra, sai ya ce wadan nan sunayen na wasu Mutanen kikrki ne daga cikin Mutanen Annabi Nuh, yayai da suka Mutu sai shaidan yayi musu wahayi ga Mutanensu kan su kafa a wurarensu da suke zama gumaka, kuma su sa musu sunansu sai kuwa suka yi, kuma ba'a bauta musu ba sai bayan wadan nan sun Mutu kuma an manta da Ilimin sai aka rika bauta musu"
Ingantacce ne - Buhari ne ya rawaito shi

Bayani

Dan Abbas yana Fassara wannan Aya mai girma cewa wadan nanGumakan wadanda aka ambata a Alkurani cewa Mutanen Annabi Nuhu ne sunyi ta yiwa junansu wasiyya da ayi ta bauta musu bayan Annabinsu ya hanasu ga barin yin Shirka da Allah, kuma cewa ita a Asali sunaye ne na Mutanen kirki daga cikinsu, wanda suka wuce gona da Iri da yadda Shaidan ya kawata Musu har suka kafa gumakansu, sai kuma al'amarin wadan Hotunan ya koma Gumaka da ake bauta musu koma bayan Allah.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Jamusanci Japananci bushtu Asami Albaniyanci
Manufofin Fassarorin