عن أبي هريرة رضي الله عنه مرفوعاً: «من كان يؤمن بالله واليوم الآخر فليقل خيرًا أو ليصْمُت، ومن كان يؤمن بالله واليوم الآخر فليُكْرِم جارَه، ومن كان يؤمن بالله واليوم الآخر فليكرم ضَيْفَه».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira - Allah ya yarda da shi - zuwa ga Annabi : " Duk wanda yai Imani da Allah da Ranar lahira to ya fadi Alkairi ko yayi shiru, kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama Makwabcinsa,kuma duk wanda yayi Imani da Allah da Ranar Lahira to ta girmama to ya girmama Bakonsa"
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- daga Annabi Tsira da Amincin Allah su tabba a gare shi ya antar cewa daga Annabi Aminci Allah a gareshi da wasu Ginshikan tubalan zamantakewa da suka hade komai sai ya ce: "Duk wanda yai Imani" wannan Jumala ce ta sharadi kuma Jawabinta shi ne to ya fadi Alkairi ko kuma ya ja bakinsa yayi shiru" kuma abinda ake nufi da ita shi ne kwadaitarwa da jan hankali akan fadin alkairi ko kuma yin shiru kamar yana cewa: indai kayi Imani da Allah da ranar lahira to ka fadi Alkairiko kayi shiru kuma imani da Allah da ranar lahira bayaninsu ya Gabata. "to ya fadi Alkairi" kamar ya fadi abin da bai mai dadi a cikin uciyarsa ba amma kuma da niyyar shigar da farin ciki ga abokan zamansa, to wannan Alkairi ne domin yana dauke da dauke kewa da kuma gusar da damuwa da samar da hadin kai. "ko kuma yayi shiru" ai ya kame bakinsa "kuma duk wanda yayi Imani da Allah da ranar lahira to ya girmama Makwabcinsa" ai Makwabcinsa na gida, kuma abunda yake bayyane ya hadar da har Makwabcinsa na Kasuwa kamar Makwacin kantinsa a Misali, sai dai a na farkon yafi bayyana shi ne Makwabcin gida kuma ko yaushe Makwabci yafi kusa da kai koyaushe hakkinsa yafi girma akanka, kuma Annabi ya saki kaidin Girmamawa sai ya ce: "to ya girmama Makwabcinsa" kuma bai ce misali a bashi Dirhami ba ko Sadaka ko tufa, ko abin da yai kama da shi, dukkan wani abu da yazo saki kaidi a shariar Musulunci to fassararsa ana komawa zuwa ga Al'adar Mutane ne, to girmamawa ba'a ware wani abu daya ba aa ya hade duk abunda Mutane suke kiransa Girmamawa, kuma wannan ya banbanta daga wannan Makwabci izuwa wani don makwabcinka Talaka wani lokacin girmamashi ka bashi Abinci ne, amma makwabcinka Mawadaci shi wannan bai isa ka girmama shi da shi ba, Makwabcin wanda ba kowa ba ya isar maka ko Dan yaya kayi masa amma kuma Makwabcinka wanda ya ya isa a Matsayi yana bukatar girmamawa ta Musamman, kuma Makwabi: wai shi ne wanda yake jikin katangarka ko kuma abokin kasuwancinka a kasuwa, ko mai kallaonka ko kuma ma waye dai? wannan ma dai za'a koma Al'ada ne Kuma amma fadi Annabi "Duk wanda yai Imani da Allah da ranar Lahira to ya girmama Bakonsa" Bako shi ne wanda ya sauka a gurinka kamar Matafiyi da ya sauka a gurinka to wannan bako ne ya wajaba ka girmamashi da duk abin da za'a kirashi girmamawa wasu daga Ma'abota Ilimi suka ce Allah yayi Musu Rahama cewa Liyafa tana wajaba idan ya kasance a kauye ne ai kananan birane, amma a manyan birane bata zama dole ba domin anan akwai gidajen Abinci da kuma wuraren sauka da mutum zai iya kamawa ya sauka amma a kauye yana da bukatar inda zai kwana sai dai abinda Hadisin yake fada ya game komai: "to ya girmama Bakonsa" [Sharhin Hadisai Arba'in Na Nawawi, Na Muhammad Bin Saleh Al'uthaimeen 9176-178)]

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Jamusanci Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin