Karkasawa: Aqida . Imani da Ranar Lahira .

عَنْ عَبْدِ اللهِ بْنِ عَمْرِو بْنِ العَاصِ رضي الله عنهما قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«إِنَّ اللهَ سَيُخَلِّصُ رَجُلًا مِنْ أُمَّتِي عَلَى رُءُوسِ الْخَلَائِقِ يَوْمَ الْقِيَامَةِ، فَيَنْشُرُ عَلَيْهِ تِسْعَةً وَتِسْعِينَ سِجِلًّا، كُلُّ سِجِلٍّ مِثْلُ مَدِّ الْبَصَرِ، ثُمَّ يَقُولُ: أَتُنْكِرُ مِنْ هَذَا شَيْئًا؟ أَظَلَمَكَ كَتَبَتِي الْحَافِظُونَ؟ فَيَقُولُ: لَا يَا رَبِّ، فَيَقُولُ: أَفَلَكَ عُذْرٌ؟ فَيَقُولُ: لَا يَا رَبِّ، فَيَقُولُ: بَلَى إِنَّ لَكَ عِنْدَنَا حَسَنَةً، فَإِنَّهُ لَا ظُلْمَ عَلَيْكَ الْيَوْمَ، فَتُخْرَجُ بِطَاقَةٌ فِيهَا: أَشْهَدُ أَنْ لَا إِلَهَ إِلَّا اللهُ وَأَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّدًا عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ، فَيَقُولُ: احْضُرْ وَزْنَكَ، فَيَقُولُ: يَا رَبِّ مَا هَذِهِ الْبِطَاقَةُ مَعَ هَذِهِ السِّجِلَّاتِ؟ فَقَالَ: إِنَّكَ لَا تُظْلَمُ، قَالَ: فَتُوضَعُ السِّجِلَّاتُ فِي كِفَّةٍ، وَالْبِطَاقَةُ فِي كِفَّةٍ، فَطَاشَتِ السِّجِلَّاتُ، وَثَقُلَتِ الْبِطَاقَةُ، فَلَا يَثْقُلُ مَعَ اسْمِ اللهِ شَيْءٌ».

[صحيح] - [رواه الترمذي وابن ماجه]
المزيــد ...

Daga Abdullahi dan Amr dan Al-Aas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"Lallai cewa Allah zai tseratar da wani mutum daga al'ummata agaban halittu a ranar Alkiyama, sai Ya bude masa fayil dinsa x asa'in da tara, kowanne fayil tamkar iya ganinka ne, sannan Ya ce: Shin kana musun wani abu daga wannan? Shin marubutaNa masu kiyayewa sun zalinceka ne? Sai ya ce: A'a ya Ubangiji, sai Ya ce: Shin kana da wani hanzari? Sai ya ce: A'a ya Ubangiji, sai (Ubangiji) Ya ce: Eh, lallai kanada wani abu kyakkyawa a wurinmu, a yau babu wani zalinci akanka, sai a fitar da wani kati a cikinsa akwai: Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah , kuma ina shaidawa cewa Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, sai ya ce: ka zo wajan ma'aninka, sai ya ce; ya Ubangiji wannan wanne katine tare da wadannan fayilillikan? Sai Ya ce; Lallai cewa kai ba za’a zalinceka ba, sai ya ce: Sai a dora fayilillikan a bangaren ma'auni , katin kuma a daya ma'aunin, sai fayililliakn su yi sauki, kuma katin ya yi nauyi, wani abu ba zai yi nauyi tare da sunan Allah ba".

Ingantacce ne - Al-Tirmithi Ya Rawaito shi

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa Allah Zai zabi wani mutum daga al'ummarsa agaban halittu , za'a kira shi dan a yi masa hisabi, sai (Ubangiji) ya bijiro masa da fayilillika casa'in da tara, su ne takardun ayyukansa wadanda ya kasance yana aikatasu a duniya, kuma tsawon kowane fayil tamkar iya ganinnka ne. Sannan Allah - mai girma da daukaka - ya cewa wannan mutumin: Shin kana musun wani abu daga abinda aka rubuta a cikin wadanannan fayilillikan? Shin Mala'ikuna masu kiyayewa masu rubutu sun zalinceka?. Sai mutumin ya ce: A'a ya Ubangiji. Sai Allah - mai girma da daukaka - ya ce: Shin kana da wani hanzari da za'a yi maka uzuri da shi daga abinda ka gabatar na ayyuka a duniya? daga kasancewarsa rafkanuwa ne, ko kuskurene ko jahilcine, Sai mutumin ya ce: A'a ya Ubangiji ba ni da wani hanzari. Sai Allah - mai girma da daukaka - ya ce: Eh, lallai kana da wani kyakkyawan aiki a wurinMu, kuma cewa babu wani zalinci akanka a yau. Ya ce: Sai a fitar da wani kati an rubutawa a ciki: Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma ina shaida cewa Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne. Sai Allah - mai girma da daukaka - ya cewa wannan mutumin: ka zo wurin ma’aunin ka. Sai mutumin ya ce, yana mai mamaki; Ya Ubangiji! Menene nauyin wannan katin tare da wadannan fayilill din ??. Sai Allah - mai girma da daukaka - ya ce: Wani zalinci ba zai afku akanka ba. Sai ya ce ; sai a dora fayilillikan a ma'aunin, katin ma a daya ma'aunin; sai ma'aunin da fayilillkan suke a ciki su yi sauki, sai ma'aunin da katin yake ciki ya rinjaya, kuma ya yi nauyi, sai Allah Ya gafarta masa.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Jamusanci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Girman kalmar Tauhidi: Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, da nauyinta a ma'auni.
  2. Fadin: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah ba ya isa da harshe kadai, babu makawa sai an san ma'anarta da kuma aiki da abinda take hukuntawa take nema.
  3. Ikhlasi da karfin Tauhidi sababi ne na kankare zunubai.
  4. Imani yana fifita da fififtar abinda ke cikin zukata na Ikhlasi, wani daga mutane zai iya fadin wannan kalmar saidai za'a yi masa azaba da gwargwadan zunubansa.