عن عائشة - رضي الله عنها-، أن أمَّ سَلَمَة، ذَكَرَت لرسول الله صلى الله عليه وسلم كَنِيسة رأتْهَا بأرض الحَبَشَةِ يُقال لها مَارِيَة، فذَكَرت له ما رأَت فيها من الصُّور، فقال رسول الله صلى الله عليه وسلم : «أولئِكِ قوم إذا مات فيهم العَبد الصالح، أو الرُّجل الصَّالح، بَنُوا على قَبره مسجدا، وصَوَّرُوا فيه تلك الصِّور، أولئِكِ شِرَار الخَلْق عند الله».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Nana Aisha cewa ummu Salama ta gayawa Annabi cewa taga wata coci a kasar Habasha, ana kiranta Mariya, sai ta fadi duk abubuwan da ta gani a can na Hotuna, sai Annabi yace: "Wadan nan Mutane idan Mutumin kirki ya mutu daga cikinsu, ko kuma Bawa nagari, sai su gina Masallaci akan Kabarinsa, kuma suyi masa wadan nan Hotunan, Wadan nan Su ne ashararen Mutane a wajen Allah"
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Ummu Salama tana bamu labarin cewa abinda ta gani a kasar habasha na coci cikin ta da hotuna kuma ta gayawa Annabiabinda ta gani a ciki na ado da hotuna abin mamaki hakan, kuma sabida girman hakan da hadarinsa ga Tauhidi Annabi ya daga kansa kuma yayi mata bayanin dalilin yin hakan na sanya Hotunan, don tsawatarwa Al'ummarsa abinda waccan ta aikata kuma ya ce: kinga wadancan wadanda kika fada su ne idan wani bawan Allah ya mutu a cikin su sai su gina Masallaci akan Kabarinsasuna yin sallah a cikinsa, kuma su yi wadan nan hotunan, kuma ya bayyana cewa wanda yayi irin haka shi ne Mafi sharrin halitta a wajan Allah , domin aikinsa yana kaiwa zuwa ga Shirka da Allah.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية
Manufofin Fassarorin