Karkasawa: Aqida . Imani da Ranar Lahira .

عَنْ ‌قَتَادَةَ رحمه الله قال:
حَدَّثَنَا ‌أَنَسُ بْنُ مَالِكٍ رَضِيَ اللهُ عَنْهُ أَنَّ رَجُلًا قَالَ: يَا نَبِيَّ اللهِ كَيْفَ يُحْشَرُ الْكَافِرُ عَلَى وَجْهِهِ؟ قَالَ: «أَلَيْسَ الَّذِي أَمْشَاهُ عَلَى الرِّجْلَيْنِ فِي الدُّنْيَا قَادِرًا عَلَى أَنْ يُمْشِيَهُ عَلَى وَجْهِهِ يَوْمَ الْقِيَامَةِ؟» قَالَ قَتَادَةُ: بَلَى وَعِزَّةِ رَبِّنَا.

[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Katada - Allah Ya yi masa rahama - ya ce:
Anas Dan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya zantar damu cewa wani mutum ya ce: Ya Annabin Allah ya za’a tashi kafiri akan fuskarsa? Ya ce: " Shin wanda ya tafiyar da shi akan kafafuwa biyu a duniya bai zama yana da iko akan ya tafiyar da shi akan fuskarsa ranar Alkiyama ba?"Katada ya ce: Eh na rantse da buwayar Ubangijinmu.

Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

An tambayi Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Ya za'a tashi kafiri akan fuskarsa a ranar Alkiyama ?! sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce; Shin yanzu wanda ya tafiyar da shi akan kafafuwa biyu a duniya bai zama mai iko akan ya tafiyar da shi akan fuskarsa a ranar Alkiyama ba?! Allah Mai ikone akan dukkan komai.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Wulakantar kafiri a ranar Alkiyama kuma zai yi tafiya akan fuskarsa.