عَنْ أَنَسِ بْنِ مَالِكٍ رضي الله عنه قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«سَوُّوا صُفُوفَكُمْ، فَإِنَّ تَسْوِيَةَ الصَّفِّ مِنْ تَمَامِ الصَّلَاةِ».

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح مسلم: 433]
المزيــد ...

Daga Anas Dan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"ku daidaita sahunku, don daidaita shahu na daga cikar sallah".

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi] - [Sahih Muslim - 433]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana umartar masu yin sallah kan su daidaita sahunsu, kuma kada sashinsu ya gabata akan sashi kada kuma ya jinkirta, kuma daidaita sahu yana daga cikar sallah , kuma karkace sahu ɓaci ne da tawaya a sallah.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Halaccin kula da dukkan abinda yake cika sallah kuma yake nisantar da ita daga tawaya.
  2. Hikimar annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a koyarwa, ta inda ya haɗa hukunci tare da dalilinsa; dan bayyanar da hikimar shar'amtawa, da nishaɗantar da rayuka akan kamantawa.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (54)