عن عمر بن الخطاب رضي الله عنه قال: قَالَ رَسُولُ الله صلى الله عليه وسلم : «إنَّ الله يَنْهَاكُمْ أَن تَحْلِفُوا بِآبَائِكم».
وَلمسلم: «فَمَن كان حَالِفا فَلْيَحْلِف بِالله أو لِيَصْمُت».
وَفِي رِوَايَةٍ قَالَ عُمَرُ رضي الله عنه قال: «فَوَالله ما حَلَفْتُ بِهَا منذ سَمِعْت رَسُولَ الله يَنْهَى عَنْهَا، ذَاكراً وَلا آثِراً».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...
An rawaito daga Umar Bn Khattab –Allah ya yarda das hi- y ace Manzon Allah SAW ya ce: “Lallai Allah ya hanaku ku rantse da Iyayenku” daga Muslim kuma: “To duk wanda zai yi rantsuwa to ya rantse da Allah, ko yayi shiru” kuma a cikin wata riwayar Umar ya ce: -Allah ya yarda das hi- ya ce: “To na rantse da Allah ban rantse dad a wani abu ba tunda naji Manzon Allah SAW ya hana hakan, ina sane ko tuntuben baki”
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi]
Manzon Allah SAW ya ji Umar –Allah ya yarda da shi- yana rantsuwa da Mahaifinsa, sai ya kirawo su yana mai daga Muryarsa da cewa: “Lallai Allah ya hanaku rantsuwa dad a Iyayenku” sai Sahabban suka bi Umarnin Manzon Allah sai suka zamanto basa yin rantsuwa said a Allah, har lokacin da Umar yake fadin cewa bai kara rantsewa dad a wanin Allah bat un lokacin da yaji Manzon Allah SAW ya hana hakan, da gangan ne ko kuma ya na bada labarin rantsuwar waninsa ne da wanin Allah.