عن البراء بن عازِب رضي الله عنهما قال: «أَمرَنا رسول الله صلى الله عليه وسلم بِسَبْعٍ، وَنَهَانَا عن سَبْعٍ: أَمَرْنَا بِعِيَادَةِ الْمَرِيضِ، وَاتِّبَاعِ الْجِنَازَةِ، وَتَشْمِيتِ الْعَاطِسِ، وَإِبْرَارِ الْقَسَمِ (أَوْ الْمُقْسِمِ)، وَنَصْرِ الْمَظْلُوم، وَإِجابة الدَّاعي، وَإِفْشاءِ السَّلامِ. وَنَهَانَا عن خَوَاتِيمَ- أَو عن تَخَتُّمٍ- بِالذَّهَب، وَعَنْ الشُّرب بِالْفِضَّة، وعن المَيَاثِر، وعن الْقَسِّيِّ، وَعن لُبْسِ الحرِيرِ، وَالإِسْتَبْرَقِ، وَالدِّيباج».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Wannan fassarar tana bukatar Karin bita da gyaran yare.

An rawaito daga Barra’u Bn Azib -Allah ya yard da su- ya ce: “ Manzon Allah SAW ya Umarce mu da abubuwa guda bakawai: ya Umarcemu da duba mara lafiya, da raka Jana’iza, da gaida mai Atishawa, da kuma sauke Rantsuwa, da kuma taimakon wanda aka Zalunta, da kuma amsa kiran Mai kira, da yada Sallama, kuma ya hana mu sanya Zoben Zinare, da sha acikin abun sha na Azurfa, da Al-Mayathir, (Shine matakalar abunda ake sanyawa a shinfidar Doki) da Al-kusai (it ace rigar da akayi tad a Duwatsu) da kuma sanya Al-harini, da Al-istabrak (Alharini mai kauri) Al-dibaj (shima Nau’I ne na Al-harini)
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Annabi ya aikaAn aiko Annabi SAW don ya cika kyawawan Hakaye, saboda haka saboda yana kwadaitarwa akan kowane irin hali da aiki na kirki, kuma yana hana kowane irin abun ki, daga cikin hakan abunda yazo a cikin wannan Hadisin na abubuwa wadanda yai Umarni da su su ne: Gaida Mara lafiya wanda a cikinsa akwai tsayuwa da hakkin Musulmai, da kuma faranta masa, da yi masa Addu’a, da kuma bin Jana’izarsa, saboda a cikinsa akwai lada mai ga wanda ya bi, da Addu’a ga Mamata a makabarta, da wa’azantuwa da daukar izina, da kuma gaida Mara lafiya,idan ya godewa Allah sai ace das hi: Allah yayi Maka Rahama, da kubutar da rantsuwar wanda ya kirawoka zuwa wani abu a halin kuma baka da komai da zai hana ka don ka cika masa rantsuwarsa, don kada ka jawo masa Kaffara ta rantsuwarsa, don ka ansa gayyatarsa kuma ka faranta ransa, da taimakon wanda aka zalunta, daga wanda ya aka zalunce shi, saboda a cikinsa akwai kautar da zalunci, da ije Mai Ta’addanci da tosheshi daga Sharri, da Hani daga Mummunan aiki, da kuma Amsawa wanda ya kiraka, saboda cikin wancan akwai kusanto da zukata, da tsarkake rayuka, a cikinsa akawai hana kadaici da sabani, to idan gayyatar ta kasance ta aure ce to amsa ta wajibi ne, idan kuma ta kasance ta waninsa ce to Mustahabi ce, kuma yada Sallama, shi shelanta tad a kuma bayyana tag a kowa da kowa, kuma it ace yin Sallama ta sunna, da kuma Addu’ar Musulmai ga junansu,, kuma sababi ne na jawo Soyayya, amma abubuwan da aka hana a cikin wannan Hadisin shi ne hana sanya Zobban Zinare ga maza, saboda acikinsa akwai Daudanci da koyi da halin Mata, da kuma kawar da Mazakuntaka, kuma hanin Shan abun sha a abu Na Azurfa saboda a cikinsa akwai barna da girman kai, kuma idan aka hana sha tare da bukatar hakan to sauran anfanuka su suka fi cancanta da haramcin, da kuma hana sanya Kaimin Doki, da Kakkauran Alharini da Sirinsa, wadan da sune Nau’in Alharini na Maza, don suna janyo karyewar mazakuntar Mutum da kuma son jin dadi wadanda sune dalilan zaman Banza, kuma Namiji ana bukatar nishadi da gyara daga gare shi da juriya da Gwarzanta, saboda ya kasance koyaushe a shirye yake da tsayuwa da Wajibinsa na kare Addininsa da iylansa da Kasarsa

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Kurdawa Portuguese Malayalam
Manufofin Fassarorin