عن أبي هريرة رضي الله عنه قال:
أَتَى النَّبِيَّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ رَجُلٌ أَعْمَى، فَقَالَ: يَا رَسُولَ اللهِ، إِنَّهُ لَيْسَ لِي قَائِدٌ يَقُودُنِي إِلَى الْمَسْجِدِ، فَسَأَلَ رَسُولَ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ أَنْ يُرَخِّصَ لَهُ فَيُصَلِّيَ فِي بَيْتِهِ، فَرَخَّصَ لَهُ، فَلَمَّا وَلَّى دَعَاهُ، فَقَالَ: «هَلْ تَسْمَعُ النِّدَاءَ بِالصَّلَاةِ؟» فَقَالَ: نَعَمْ، قَالَ: «فَأَجِبْ».

[صحيح] - [رواه مسلم]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce:
Wani mutum makaho ya zo wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Ya Ma’aikin Allah! Ba ni da mai jagora da zai ja ni zuwa Masallaci, sai Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da ya yi masa rangwane da ya yi Sallah a gidansa, sai ya yi masa rangwame, a lokacin da ya juya ya tafi, sai ya kira shi ya ce: shin kana jin kiran Sallah idan aka kira, ya ce: Eh, sai ya ce: Ka amsa.

Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

Wani mutum makaho ya zo wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Ya Ma’aikin Allah ! Ba ni da wanda zai taimaka min ya riƙe hannuna zuwa Masallaci a salloli biyar, yana son Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi masa rangwamen sallar jam’i, sai ya yi masa rangwamen, lokacin da ya juya ya tafi, sai ya kira shi, ya ce; Shin kana jin kiran Sallah? Ya ce; Eh, ya ce: Ka amsawa mai kiran Sallah.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Wajibcin Sallar jam’i, domin rangwame ba ya kasancewa sai a abin da yake dole.
  2. Faɗinsa: "Ka amsa". Wannan ga wanda yake jin kiran sallah, yana nuna Wajibcin sallar jam’i, domin asali a umarni shi ne Wajibci.