عن جابر بن عبد الله رضي الله عنهما عن النبي صلى الله عليه وسلم أنه قال: «من أكل ثومًا أو بصلًا؛ فَلْيَعْتَزِلْنَا -أَوْ لِيَعْتَزِلْ مسجدنا-، وليقعد في بيته. وأُتي بِقِدْرٍ فيه خَضِرَاتٌ من بُقُولٍ، فوجد لها ريحًا، فسأل فأخبر بما فيها من البقول، فقال: قَرِّبُوهَا إلى بعض أصحابي، فلما رآه كره أكلها، قال: كل؛ فإني أُنَاجِي من لا تُنَاجِي». عن جابر بن عبد الله رضي الله عنهما أن النبي صلى الله عليه وسلم قال: «من أكل الثوم والبصل والْكُرَّاثَ فلا يقربن مسجدنا؛ فإن الملائكة تَتَأَذَّى مما يَتَأَذَّى منه بنو آدم».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Jabir Dan Abdullahi -Allah ya yarda da su- daga Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- yace: "Duk wanda ya ci tafarnuwa ko albasa. to sai yayi nesa damu -ko yayi nesa da masallacinmu-,sai ya zauna a gidansa.Sai aka zo da wata tukunya mai dauke da kayan marmari masu kwallaye,sai yaji wani irin wari na fitowa daga tukunyar,sai ya tambaya?sai aka bashi labarin irin abubuwan da ke ciki.sai yace: ku matsa da ita wajen sahabbai na.yayin da yaga abin da ke ciki sai yaki ci. Sai yace: ku ci. don ni ina ganawa da wanda baku ganawa da shi". Daga Jabir Dan Abdullahi Allah ya yarda da su- cewa: Annabi -tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi- yace: "Duk wanda ya ci tafarnuwa ko albasa ko kurath to kar ya kusanci masallacinmu,don mala'iku suna cutuwa da irin abin da 'yan'adam ke cutuwa da shi.
Ingantacce ne - Buhari da Muslim suka rawaito shi da ruwayoyin sa

Bayani

Abin da ake so da masallaci shi ne ya kasance cikin kyakkyawar kama da kanshi,musamman idan yana son yin salla a gurin da mutane ke haduwa.Don haka Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya umarci duk wanda yaci tafarnuwa ko albasa danyu, da yayi nesa da masallacin musulmi,yayi sallarsa a gidansa,har zuwa lokacin da warin zai sane,masllata da mala'iku makusanta suna cutuwa daga warin. Lokacin da aka zowa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- da wata tukunya ta korran kayan marmari, sai yaji wani wari marar dadi,sai yayi umarni da a matsar da su wajen wasu daga sahabban da ke tare da shi,da suka ga irin kin Annabi da wannan abu sai suka yi tsammanin cin su ya haramta,sai suke kai komo akai,sai Annabi yace ba haramun bane,kuma ba yana kin ta saboda haramci bane.kuma mai so ya ci sai ya ci,sai dai mutum ya san cewa yaki ci ne saboda ganawa da Ubangijinsa,ba wanda ke irin wannan gani da Allah sai shi,don haka ya kamata ya zama cikin kyakkyawan kamanni wajen kusantar Ubangijinsa Madaukaki,kuma kula da abin da ya shafi gaba dayan mutane ya fi kallon abin da ya shafi mutum daya kadai na halartar jam'insa.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin