+ -

عن سعد بن عبادة رضي الله عنه أنه قال:
يَا رَسُولَ اللَّهِ، إِنَّ أُمَّ سَعْدٍ مَاتَتْ، فَأَيُّ الصَّدَقَةِ أَفْضَلُ؟، قَالَ: «الْمَاءُ»، قَالَ: فَحَفَرَ بِئْرًا، وَقَالَ: هَذِهِ لِأُمِّ سَعْدٍ.

[حسن بمجموع طرقه] - [رواه أبو داود والنسائي وابن ماجه] - [سنن أبي داود: 1681]
المزيــد ...

Daga Sa'ad ɗan Ubada - Allah Ya yarda da shi - cewa shi ya ce:
Ya Manzon Allah, lallai Ummu Sa'ad ta rasu, to wace sadaka ce tafi?. Ya ce: "Ruwa". Ya ce: Sai ya haƙa wata rijiya, ya ce: Wannan ga Ummu Sa'ad ce.

- [Abu Daud Ya Rawaito shi] - [سنن أبي داود - 1681]

Bayani

Mahaifiyar Sa'ad ɗan Ubada - Allah Ya yarda da shi - ta rasu, sai ya tambayi Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - game da mafificin nau'ikan sadaka dan ya yi sadaka dashi ga mahaifiyarsa? sai tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ba shi labarin: Cewa mafificiyar sadaka ita ce ruwa, sai ya haƙa wata rijiya ya sanyata sadaka ga mahaifiyarsa.

Fassara: Indonisiyanci Sinhalese Vietnam Tagalog Swahili bushtu Asami الأمهرية الهولندية الغوجاراتية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Bayanin cewa ruwa yana daga mafificin nau'ikan sadaka.
  2. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya nunawa da Sa'ad zuwa ga sadakar ruwa; domin shi ya fi gamewar anfani a cikin al'amuran addini da duniya, kuma saboda tsananin zafi da buƙata da ƙarancin ruwa.
  3. Nuni akan ladan sadaka yana zuwa ga mamata.
  4. Biyayyar Sa'ad ɗan Ubada - Allah Ya yarda da shi - ga mahaifiyarsa - Allah Ya yarda da su -.