+ -

عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ رضي الله عنه قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«لَا تَدْخُلُونَ الْجَنَّةَ حَتَّى تُؤْمِنُوا، وَلَا تُؤْمِنُوا حَتَّى تَحَابُّوا، أَوَلَا أَدُلُّكُمْ عَلَى شَيْءٍ إِذَا فَعَلْتُمُوهُ تَحَابَبْتُمْ؟ أَفْشُوا السَّلَامَ بَيْنَكُمْ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 54]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce:
"Ba za ku shiga aljanna ba har sai kun yi imani, Ba za ku yi imani ba har sai kun so junanku, , shin ba na shiryar daku akan abinda idan kun aikata shi za ku so junanku ba? ku yada sallama a tsakaninku".

Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agar shi - ya bayyana cewa ba masu shiga aljanna sai muminai, kuma imani ba ya cika, sannan halin jama'ar musulmai ba ya gyaruwa har sai sashinsu yaso sa shi. Sannan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agar shi - ya shiryar zuwa mafificin al'amuran da su ne soyayya take gamewa, ita ce yada sallama tsakanin musulmai, wacce Allah Ya sanyata gaisuwa ga bayinSa.

Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Kurdawa Portuguese Telgonci Swahili Yaran Tailand bushtu Asami السويدية الأمهرية الغوجاراتية القيرقيزية النيبالية اليوروبا الدرية الصومالية الكينياروندا التشيكية المالاجاشية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Shiga aljanna ba ya kasancewa saida imani.
  2. Daga cikar imani musulmi ya so wa dan uwansa abinda yake sowa kansa.
  3. An so yada sallama da shinfidata ga musulmai; dan abinda ke cikinta na yada soyayya da aminci tsakanin mutane.
  4. Ba'ayin sallama sai ga musulmi; saboda fadinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agar shi -: "A tsakaninku".
  5. Yada sallam Akwai dauke damuwa da kauracewa da gaba ta hanyar yin sallama.
  6. Muhimmancin soyayya tsakanin musulmai, kuma cewa ita tana daga cikar imani.
  7. Ya zo a cikin wani hadisin daban cewa sigar sallama cikakkiya: "Assalamu alaiku warahmatullahi wa barakatuh ", ya isa a ce: "Assalamu alaikum".