+ -

عَنْ عَبْدِ اللهِ بْنِ مُغَفَّلٍ رضي الله عنه قَالَ: قَالَ النَّبِيُّ صلى الله عليه وسلم:
«بَيْنَ كُلِّ أَذَانَيْنِ صَلَاةٌ، بَيْنَ كُلِّ أَذَانَيْنِ صَلَاةٌ» ثُمَّ قَالَ فِي الثَّالِثَةِ: «لِمَنْ شَاءَ».

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 627]
المزيــد ...

Daga Abdullahi dan Mugaffal - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"A kwai sallah tsakanin dukkan kiran sallah biyu, akwai sallah tsakanin dukkan kiran sallah biyu" sannan ana uku ya ce: "Ga wanda ya so".

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح البخاري - 627]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa akwai sallar nafila tsakanin kowanne kiran sallah da iƙama, kuma ya maimaita hakan sau uku, kuma ya bada bayani ana ukun cewa hakan mustahabbi ne ga wanda ya yi nufin yin sallah.

Fassara: urdu Indonisiyanci Sinhalese Vietnam Tagalog Swahili bushtu Asami الأمهرية الهولندية الغوجاراتية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. An so sallah tsakanin kiran sallah da iƙama.
  2. Shiriyar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a maimaita magana, hakan dan jiyarwa da ƙarfafawa ga muhimmnacin abinda yake faɗa.
  3. Abin nufi da kiran sallah biyu: Kiran sallah da iƙama, kuma ya anbace su da (lafazin) (Kiran sallah biyu) dan rinjayarwa, kamar wata biyu (Rana da wata) da Umar biyu (Abubakar da Umar).
  4. Kiran sallah shi ne sanar da shigar lokaci, iƙama kuma ita ce sanar da halartar yin sallah.