+ -

عَنْ ‌حُمْرَانَ مَوْلَى عُثْمَانَ بْنِ عَفَّانَ أَنَّهُ رَأَى عُثْمَانَ بْنَ عَفَّانَ دَعَا بِوَضُوءٍ، فَأَفْرَغَ عَلَى يَدَيْهِ مِنْ إِنَائِهِ، فَغَسَلَهُمَا ثَلَاثَ مَرَّاتٍ، ثُمَّ أَدْخَلَ يَمِينَهُ فِي الْوَضُوءِ، ثُمَّ تَمَضْمَضَ وَاسْتَنْشَقَ وَاسْتَنْثَرَ، ثُمَّ غَسَلَ وَجْهَهُ ثَلَاثًا، وَيَدَيْهِ إِلَى الْمِرْفَقَيْنِ ثَلَاثًا، ثُمَّ مَسَحَ بِرَأْسِهِ، ثُمَّ غَسَلَ كُلَّ رِجْلٍ ثَلَاثًا، ثُمَّ قَالَ: رَأَيْتُ النَّبِيَّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَتَوَضَّأُ نَحْوَ وُضُوئِي هَذَا، وَقَالَ: «مَنْ تَوَضَّأَ نَحْوَ وُضُوئِي هَذَا ثُمَّ صَلَّى رَكْعَتَيْنِ لَا يُحَدِّثُ فِيهِمَا نَفْسَهُ غَفَرَ اللهُ لَهُ مَا تَقَدَّمَ مِنْ ذَنْبِهِ».
[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 164]
المزيــد ...

Daga Humran bararran bawa na Usman Dan Affan cewa ya ga Usman Dan Affan ya nemi da akawo masa ruwan alwala, sai ya karkato da kwaryar (butar Alwala), sai ya wankesu sau uku, sannan ya shigar da (hannunsa na) dama a ruwan alwalar, sannan ya kuskure baki ya shaƙa ruwa ya face, sannan ya wanke fuskarsa sau uku, da hannayensa zuwa gwiwar hannaye sau uku, sannan ya shafi kansa, sannan ya wanke kowacce ƙafa sau uku, sannan ya ce: Na ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a greshi - ya yi alwala irin wannan alwalar tawa, sai ya ce: "Wanda ya yi alwala irin wannan alwalar tawa sannan ya yi sallah raka'a biyu bai zantar da ransa a cikinsu ba, to, Allah Zai gafarta masa abin da ya gabata daga zunubinsa".
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Sayyidina Usman - Allah Ya yarda da shi - ya karantar da siffar alwalar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a aikace; don ya zama mafi fitowa ɓaro-ɓaro, sai ya nemi ruwa a ƙwarya, sai ya zuba a hannayensa sau uku, bayan haka ya shigar da hannunsa na dama a cikin ƙwaryar, sai ya ɗebo ruwa daga cikinta sai ya kurkura shi a bakinsa, sannan ya fitar da shi, sannan ya shaki ruwan da numfashinsa zuwa cikin hancinsa, sannan ya fitar da shi ya face, sannan ya wanke fuskarsa sau uku, sannan ya wanke hannayensa tare da gwiwar hannaye sau uku, sannan ya shuɗar da hannunsa a kan kansa suna masu damshi da ruwa sau ɗaya, sannan ya wanke ƙafafuwansa tare da idon sawu sau uku.
Lokacin da ya gama - Allah Ya yarda da shi - sai ya ba su labarin cewa shi ya ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi - ya yi alwala irin wannan alwalar, kuma [Annabi] - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi musu albishir da cewa wanda ya yi irin wannan alwalar, ya yi sallah raka'a biyu, yana mai khushu'i yana mai halarto da zuciyarsa a gaban Ubangijinsa - mai girma da ɗaukaka - a cikinsu, to, Allah Zai yi masa sakayya a kan wannan alwalar cikakkiya da wannan sallar tsarkakiyya da gafarta abin da ya gabata daga zunubansa.

Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Jamusanci Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية القيرقيزية النيبالية اليوروبا الليتوانية الدرية الصومالية الكينياروندا التشيكية المالاجاشية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. An so wanke hannaye kafin shigar da su a cikin ƙwarya (butar Alwala) a farkon alwala, ko da bai kasance ya taso daga barci ba, idan ya farka daga barcin dare ne, to, ya wajaba a wankesu.
  2. Ya kamata ga mai koyarwa ya bi hanya mafi kusa ga fahimta da tabbatar da ilimi ga mai koyo, daga hakan akwai koyarwa a aikace.
  3. Ya kamata ga mai sallah ya tunkuɗe duk wasu tunani dake rataye da shagulgulan duniya, cikar sallah da kamalarta (yana tabbata ne) a halartowar zuciya a cikinta, in ba haka ba fa, to, kuɓuta daga tunani iri daban daban yana da wahala [a sallah], ya wajaba a kansa ya yaƙi ransa kada ya yi sako-sako a hakan.
  4. An so damantawa a alwala.
  5. Shar’antuwar jerantawa a tsakanin kuskurar baki da shaƙa ruwa da facewa.
  6. An so wanke fuska da hannaye da ƙafafuwa sau uku, amma wajibi (shi ne) sau ɗaya.
  7. Gafarar Allah ga abin da ya gabata daga zunubai ya jerantu ga al'amura biyu: Alwala, da sallah raka'a biyu, a kan siffar da aka ambata a hadisin.
  8. A kwai iyaka ga kowacce gaɓa daga gaɓɓan alwala: Iyakar fuska:
  9. Tun daga matsirar gashin kai na al'ada, zuwa abin da ya sauka zuwa gemu da haɓa a tsawo, a faɗi kuma daga kunne zuwa kunne. Iyakar hannu: Tun daga gefen 'yan yatsu zuwa gwiwar hannu, shi ne mararraba tsakanin sangalalin hannu da damtse.
  10. Iyakar kai kuma: tun daga matsirar gashi na al'ada daga sasannin fuska zuwa saman wuya, shafar kunnuwa suna cikin kai. Iyakar ƙafa: Dudduge gabaɗayansa tare da mararraba tsakaninsa da ƙwauri.