+ -

عن صُهيب بن سِنان الرومي رضي الله عنه مرفوعاً: «عجَبًا لِأَمر المُؤمِن إِنَّ أمرَه كُلَّه له خير، وليس ذلك لِأَحَد إِلَّا لِلمُؤمِن: إِنْ أَصَابَته سَرَّاء شكر فكان خيرا له، وإِنْ أَصَابته ضّرَّاء صَبَر فَكَان خيرا له».
[صحيح] - [رواه مسلم]
المزيــد ...

Daga Suhaib - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce -:
’’Lamarin mumini da ban mamaki yake, dukkannin al’amuransa alheri ne, kuma hakan ba ya kasancewa ga kowa sai ga mumini ,idan abin farinciki ne ya same shi sai ya gode wa Allah sai, sai ya zamar masa alheri, idan kuma na sharri ne ya same shi sai ya yi haƙuri, shi ma sai ya zamar masa alheri’’.

Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

(Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi yana mamaki daga sha'anin mumini da halayensa ta ɓangaren kyautatawa; hakan domin halayensa dukkansu alheri ne, kuma hakan ba ya kasancewa ga wani sai ga mumini; Idan farin ciki ya same shi sai ya godewa Allah; sai ya samu lada saboda godiyarsa. Idan kuma cuta ta same shi sai ya yi haƙuri ya nemi lada a wurin Allah, sai ya samu lada saboda haƙuri, shi a kowanne hali yana cikin lada.

Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Swahili Yaran Tailand Asami السويدية الأمهرية القيرقيزية اليوروبا الدرية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Falalar godiya akan farin ciki da kuma haƙuri akan cuta, wanda ya aikata hakan alherin duniya da na lahira za su same shi, wanda bai godewa ni'ima ba, kuma bai yi haƙuri akan musiba ba, to lada ya wuce shi, kuma zai samu zunubi.
  2. Falalar imani, kuma cewa lada a kowanne hali ba ya kasancewa sai ga ma'abota imani.
  3. Godiya a lokacin farin ciki, da haƙuri akan cuta suna daga ɗabi'un mumini.
  4. Imani da hukuncin Allah da kuma ƙaddararSa yana sanya mumini a cikin cikakkiyar yarda a kowanne halinsa, saɓanin wanin mumini wanda yake kasancewa a cikin fushi, idan ya sami Ni’ima daga Allah madaukakin sarki sai ya shagalta da ita daga biyayya ga Allah, amadadin haka ma sai ya juyar da ita a saɓonSa.