عن أبي رقية تميم بن أوس الداري رضي الله عنه أن النبي صلى الله عليه وسلم قال: «الدين النصيحة» قلنا: لمن؟ قال: «لله، ولكتابه، ولرسوله، ولأئمة المسلمين وعامتهم».
[صحيح] - [رواه مسلم]
المزيــد ...

Daga Tamim Dan Aus Al-dari -Allah ya yarda da shi- cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce: "Addini Nasiha ne" Muka ce ga wa ? Ya ce: "Ga Allah kuma ga Littafinsa, kuma ga Manonsa, kuma ga Jagororin Musulmi da sauran Mutane baki daya"
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

Addinin Gaskiya yazo da tsarkake Nasiha da kuma yinta kuma cewa muyi Imani kuma muna Ikrari da kadaita Allah, kuma muna tsarkake shi daga dukkan tawaya, kuma muna sifanta shi da dukkan Sifar Kamala, kuma cewa Al'kur'ani Zancensa ne kuma ya ya sauka da shi ba kuma abin halitta bane, kuma muna yin aiki da duk hukuncin dake cikinsa, kuma muna imani da duk abinda bamu fahimci Ma'anarsa ba a cikinsa, kuma mungasgata Manzo da abinda ya zo da shi, kuma muna kokarin aikata duk abinda ya Umarce mu, kuma muna nisanta daga duk abinda ya hane mu, kuma munayin Nasiha ga Shugabannin Musulmi zuwa gaskiya, kuma kamewa ga barin cutar da su haka muna kare musu cutar Wasun su ma gwargwadon iko, kuma muna Umartarsu da kyakkyawan aiki kuma muna hanasu mummunan aiki, kuma abu a dunkule da muke musu na Nasiha shi ne, Cewa Muna so musu duk abinda Muke so a kankin kanmu.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tamili Yaran Barma Yaran Tailand Jamusanci Japananci bushtu Asami Albaniyanci السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin