+ -

عَنْ عَائِشَةَ أُمِّ المؤْمنينَ رَضيَ اللهُ عنها:
أَنَّ النَّبِيَّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ كَانَ إِذَا خَرَجَ مِنَ الغَائِطِ قَالَ: «غُفْرَانَكَ».

[صحيح] - [رواه أبو داود والترمذي وابن ماجه وأحمد] - [سنن أبي داود: 30]
المزيــد ...

Daga Nana Aisha Uwar Muminai - Allah Ya yarda da ita -:
Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan ya fito daga bayan gida yana cewa: "Ina neman gafararKa".

[Ingantacce ne] - [Ibnu Majah ne ya Rawaito shi - Buhari ne ya rawaito shi - Al-Tirmithi Ya Rawaito shi - Abu Daud Ya Rawaito shi - Ahmad ne ya rawaito shi - Al-Darumi Ya Rawaito shi] - [سنن أبي داود - 30]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan ya fito daga biyan buƙatarsa na bayan gida yana cewa: Ina roƙonKa (gafararKa) ya Allah.

Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Swahili bushtu Asami الأمهرية الهولندية الغوجاراتية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. An so faɗin: "Ina neman gafafarKa" bayan fitowa daga wurin biyan buƙata.
  2. Neman gafarar da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi ga Ubangijinsa a dukkanin halaye.
  3. An ce: A cikin sababin neman gafara bayan biyan buƙata: Don taƙaitawa ne a cikin godiyar ni'imomin Allah masu yawa , daga cikinsu akwai sawwaƙa fitar abinda yake cutarwa, kuma ina neman gafararKa dan na shagalta daga anbatanKa a lokacin biyan buƙata.