عن بريدة رضي الله عنه قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم:
«إِنَّ الْعَهْدَ الَّذِي بَيْنَنَا وَبَيْنَهُمُ الصَّلَاةُ، فَمَنْ تَرَكَهَا فَقَدْ كَفَرَ».

[صحيح] - [رواه الترمذي والنسائي وابن ماجه وأحمد] - [سنن النسائي: 463]
المزيــد ...

Daga Buraidah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce -:
"Lallai alƙawarin da ke tsakanin mu da su (shi ne) sallah, wanda ya barta, to, haƙiƙa ya kafirta".

[Ingantacce ne] - [Tirmizi da Nasa'i da Ibnu Majah da Ahmad ne Suka rawaito shi] - [Sunanu Nasa'i - 463]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana bayyana cewa alƙawari tsakanin musulmai da wasunsu daga kafirai da munafikai (shi ne) sallah, wanda ya barta to haƙiƙa ya kafirta.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Girman al'amarin sallah, kuma cewa ita ce mai banbantawa tsakanin mumini da kafiri.
  2. Tabbatar da hukunce-hukuncen musulunci da zahiri daga halin mutum ba baɗininsa ba.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (57)