عن أبي واقد الليثي رضي الله عنه قال: خَرَجْنا مع رسول الله صلى الله عليه وسلم إلى حُنَيْنٍ ونحن حُدَثاءُ عَهْد بكُفْرٍ، وللمشركين سِدْرَةٌ يَعْكُفُون عندَها، ويَنُوطُون بها أسلحتهم، يُقَالُ لها: ذاتُ أَنْوَاطٍ، فمَرَرْنا بسِدْرَةٍ فقلنا: يا رسول الله، اجعل لنا ذاتَ أَنْوَاطٍ كما لهم ذاتُ أَنْواطٍ؛ فقال رسول الله صلى الله عليه وسلم : «الله أكبر، إنها السُّنَنُ! قلتم والذي نفسي بيده كما قالت بنو إسرائيل لموسى: {اجْعَلْ لَنَا إِلَهًا كَمَا لَهُمْ آلِهَةٌ قَالَ إِنَّكُمْ قَوْمٌ تَجْهَلُونَ} لتَرْكَبُنَ سُنَنَ من كان قَبْلَكم».
[صحيح] - [رواه الترمذي وأحمد]
المزيــد ...

An karbo daga Abi waqidil-laithi Allah ya yarda da shi ya ce: mun fita tareda manzon Allah mai tsira da aminchi su tabbata a gareshi zuwa Hunaini a wannan lokacin bamu dade da fita daga kafirchi zuwa musulunchi ba, su kuma mushirikai suna da wata bishiyar magarya da suke bautata mata,kuma suna rataye takubban su a jikinta, ana kiranta da suna zatu anwadin. sai muka wuce ta wannan bishiyar magarya sai mukace: ya manzon Allah, ka sanya mana ma`abociyar albarka kamar yadda wadannan mushirikai suke da ma`abociyar albarka; sai manzon Allah mai tsira da aminchi ya ce: [Allahu Akbar ! lallai ita tafarkai ce , na rantse da wanda rayuwata ke hannunsa kun fadi kamar yadda banu isra`ila suka fada ga musa: { ka sanyamana abin bauta kamar yadda suke da abin bauta, ya cemusu kudai mutane ne jahilai } Na rantse da Allah sai kun hau tafarkan wadanda suka gabace ku}}
Ingantacce ne - Al-Tirmithi Ya Rawaito shi

Bayani

Abu waaqidillaisi Allah ya qara yarda a gareshi yana bada labari gameda faruwar wani al-amari wanda ke cike da mamaki da wa`azantarwa: wannan waaqi`ah ita ce cewa sun fita yaki tareda manzon Allah mai tsira da aminchi su kara tabbata a gareshi zuwa kabilar Hawazin,a wannan lokacin basu jima da shiga musulunchi ba; sai al-amarin shirka ya buya a garesu, a lokacin da suka ga abinda mushirikai suke aikatawa na neman albarka daga bishiyar da suke bauta sai suka nemi manzon Allah metsira da aminchi da ya sanya musu bishiya irinta don su bautata mata, Sai annabi mai tsira da aminchi su kara tabbata a gareshi yayi kabbara yana mai inkarin abinda suka nema, tareda girmamawa ga Allah madaukaki, yana mai cike da mamakin wannan magana tasu, sa`annan ya basu labarin cewa wannan magana tasu tayi kama da maganar mutanen annabi musa a lokacin da suka ga masu bautar gumaka sai suka cewa annabi musa: {ka sanya mana abin bauta kamar yadda wadannan suke da abin bauta}. kuma wannan shi ne bin irin tafarkin su, sa`annan mai tsira da aminchi ya bada labarin cewa wannan al-ummar tasa lallai sai tabi tafarkin yahudu da nasara, kuma sai sunyi riko da irin tsarin su, sai sun aikata irin abinda suka aikata, shi wannan labarin ma`anar sa shi ne: nuna zargi da tsoratarwa daga irin wannan aiki na shirka.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Swahili bushtu Asami السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin