عن أبي موسى الأشعري رضي الله عنه قال: «سُئِلَ رَسُولُ الله صلى الله عليه وسلم عَنْ الرَّجُلِ: يُقَاتِلُ شَجَاعَةً، وَيُقَاتِلُ حَمِيَّةً، وَيُقَاتِلُ رِيَاءً، أَيُّ ذَلِكَ فِي سَبِيلِ الله؟ فَقَالَ رَسُولُ الله صلى الله عليه وسلم : مَنْ قَاتَلَ لِتَكُونَ كَلِمَةُ الله هِيَ الْعُلْيَا، فَهُوَ فِي سَبِيلِ الله».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abu Musa Al'ash'ary- Allah ya yarda da shi- yace: "An tambayi Manzon Allah game da mutumin da ke yaki don jarumta, ko dan kabilanci, ko dan riy
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Wani mutum ya tambayi Annabi tsira da amincin Allah game da mutumin da ke yakar makiya addini, amma yana yi ne don ya nuna jarumta, da kuma wucewa gaba a fagen yaki, da wanda ke yaki don kabilanci, na ukuk kuma yana yaki ne don ya nunawa mutane shi jarumi ne ya cancanci a yaba masa. To a cikinsu wa yake yi don Allah? Sai Manzo tsira da amincin Allah ya amsa da takaitacciyar magana mai dauke da tarin ma'ana, itace: Wanda ya yi yaki don kalmar Allah ta daukaka, duk wanda ba haka bane, to ba don Allah yake yi ba, yana yi ne don wata manufa. Ayyuka kuma suna bin niyyoyi ne wajen kyau da inganci ko awajen baci, wannan kuwa ya game dukkanin ayyuka abin da ke tasiri cikinsu shi ne niyya , wajen kyautatuwarsu ko bacinsu, dalilan da ke nuna haka suna da yawa.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Swahili
Manufofin Fassarorin