عن عَبْدُ الله بن عمر رضي الله عنهما «أَنَّ امْرَأَةً وُجِدَتْ فِي بَعْضِ مَغَازِي النَّبِيِّ صلى الله عليه وسلم مَقْتُولَةً، فَأَنْكَرَ النَّبِيُّ صلى الله عليه وسلم قَتْلَ النِّسَاءِ، وَالصِّبْيَانِ».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Abdullahi dan umar- Allah ya kara yarda a garesu su biyun- { Cewa tabbas an sami wata mata da aka kashe a cikin wani sashi daga cikin yakokin annabi mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi, sai annabi mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi yayi inkarin kashe mata, da yara }.
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

Hanin annabi mai tsira da amincin Allah su kara tabbata a gareshi da yayi na kashe mata da yara yana nuninbisa haramcin kashe su, fadar sa a cikin wani sashin hadisan da suka zo cikin wannan ma`ana: (Bai dace wannan dai tayi yaki ba) fadakarwa ce bisa illar hani dangane da hana kashe mata; saboda mafi rinjaye a cikin su basa yin yaki duk da kasancewar wasu a cikin su suna da sharri da jarumta saidai hukuncin an rataya shi bisa mafi rinjayensu, amma duk wadda tayi yaki a cikin su sai a yake ta.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Swahili
Manufofin Fassarorin