عَن أَبِي سَعِيدٍ الْخُدْرِيِّ رضي الله عنه قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«إِذَا تَثَاءَبَ أَحَدُكُمْ فَلْيُمْسِكْ بِيَدِهِ عَلَى فِيهِ، فَإِنَّ الشَّيْطَانَ يَدْخُلُ».

[صحيح] - [رواه مسلم] - [صحيح مسلم: 2995]
المزيــد ...

Daga Abu Sa'idul Khudri - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce:
"Idan ɗayanku zai yi hamma to ya riƙe bakainsa da hannunsa, domin cewa Shaiɗan yana shiga".

[Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [Sahih Muslim - 2995]

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fadakar da wanda zai yi hamma cewa buɗe bakinsa saboda kasala ce ko cika ko wanin haka; cewa ya ɗora hannunsa akan bakinsa sai ya rufeshi da shi; hakan domin Shaiɗan yana shiga cikinsa idan ya barshi a buɗe, to ɗora hannu yana zama mai hana shigarsa.

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Idan mutum yana son yin hamma to ya wajaba a kansa ya rufe (bakinsa) daidai iko, cewa ya riƙe bakinsa, sai ya barshi a rufe ta inda ba zai buɗe ba, idan ba zai iya barin bakinsa a rufe ba to ya ɗora hannunsa akan bakinsa, sai ya rufe bakinsa da hannunsa.
  2. Lazimtar ladubban Musulunci a dukkan halaye; domin cewa sune alamomi na cika da kuma ɗabi'u.
  3. Kiyayewa daga dukkan mashigar Shaiɗan ga mutum.
Manufofin Fassarorin
Yare: Turanci urdu Sifaniyanci Kari (42)