عن أبي هريرة رضي الله عنه عن النبي -صلى الله عليه وآله وسلم- قال: «مَن نَفَّسَ عن مؤمنٍ كُرْبَةً من كُرَبِ الدُّنيا نَفَّسَ اللهُ عنه كُرْبَةً من كُرَبِ يومِ القِيَامَة، ومن يَسَّرَ على مُعْسِرٍ يَسَّرَ اللهُ عليه في الدُّنيا والآخرةِ، ومن سَتَرَ مُسْلِمًا سَتَرَهُ اللهُ في الدُّنيا والآخرةِ، واللهُ في عَوْنِ العَبْدِ ما كَانَ العبدُ في عَوْنِ أَخِيهِ، ومن سَلَكَ طَرِيقًا يَلتَمِسُ فِيهِ عِلمًا سَهَّلَ اللهُ له به طريقًا إلى الجنةِ، وما اجْتَمَعَ قَوْمٌ في بيتٍ من بيوتِ اللهِ يَتْلُونَ كتابَ اللهِ ويَتَدَارَسُونَهُ بينهم إلا نَزَلَتْ عليهم السَّكِينَةُ وغَشِيَتْهُمُ الرَّحْمَةُ وحَفَّتْهُمُ الملائِكَةُ، وذَكَرَهُمُ اللهُ فِيمَنْ عِندَهُ، ومَن بَطَّأ به عمله لم يُسرع به نَسَبُهُ».
[صحيح] - [رواه مسلم]
المزيــد ...

Daga Abu Huraira zuwa ga Annabi: "Duk wanda ya yayewa Mumini wani Bakin ciki na daga bakin cikin Duniya to Allah zai yaye Masa bakin cikin lahira, kuma duk wanda ya yalwatawa wanda yake cikinMatsuwa to Allah zai yalwata Masa a Duniya da Lahira, kuma duk wanda ya Suturta wani Musulmi to Allah zai Suturtashi a Duniya da Lahira, kuma duk wanda ya suturta Mumini to Allah shima zai Suturtashi a ranarDuniya da lahira, kuma Allah yana taimakon bawa Matukar Bawa yana taimakon Dan'uwansa, kuma duk wanda ya kama wata hanya yana neman Ilimi a cikinta to Allah zai sawwake masa hanyar shiga Aljanna, kuma Mutane basu taru ba a daki daga cikin dakunan Allah suna karanta littafin Allah sai Allah ya saukar musu da Nutsuwa akansu, kuma Rahama ta lullubesu, kuma Mala'iku sun kewaye su, kuma Allah ya Ambace su cikin wadanda suke tare da shi, kuma duk wanda ya duk aikin da Dakire shi to Nasabarsa bazata sa yayi gaba ba.
Ingantacce ne - Muslim ne ya rawaito shi

Bayani

Wannan Hadisi Mai girma yana nuna mana : cewa duk wanda ya yayewa Musulmi wani bacin rai daga cikin Bacin ran Duniya , ko kuma ya Saukake masa abu mai wuya a gare shi, ko ya suturta masa wani kuskure ko wata zamiya to Allah zai saka Masa da irin aikin da yayi na amfani, kuma cewa Allah Madaukaki zai taimaki bawa da dacewa a Duniya da Lahira duk lokacin da yake taimakawa Dan Uwansa Musulmi akan wasu abubuwa masu wuya a gare shi, kuma duk wanda ya kama wata ta zahiri kamar tafiya zuwa Majalisin Ambaton Allah Allah ko Majalisin Malamai Masana kuma Masu aiki da Ilimin Nasuda niyyar neman Ilimi , ko kuma ya kama wata hanyar ta boye wacce zata kaishi ga samun Ilimi kamar bitar karatun da karance karance, ko kuma tunaninsa ko kuma fahimtarsa da abunda ake koya Masa na Ilimai Mai Amfani wanda zai kai shi zuwa Aljannah, kuma wadanda suka taru a wani daki daga cikin Daku nan Allah domin Karanta Alqur'ani Mai girma da kuma koyar da shi a tsakaninsu Allah zai basu Nutsuwa da kuma lullubewar Rahama , da kuma halartar Mala'iku da kuma yabo a garesu daga Allah a cikin Mutane Mafi daukaka, kuma cewa kowane irin girma yana samuwa ne da aikin kwarai ba da dangantaka ta jini ko kuma ta Matsayi.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese
Manufofin Fassarorin