عن جابر بن عبد الله رضي الله عنهما أنّ النبيَّ صلى الله عليه وسلم قال: «أُعْطِيتُ خمسا، لم يُعْطَهُنَّ أحد من الأنبياء قبلي: نُصِرْتُ بالرعب مسيرة شهر، وجُعِلَت لي الأرض مسجدا وطَهُورا، فأَيَّمَا رجل من أمتي أدركته الصلاة فَلْيُصَلِّ، وأُحِلَّت لي المغانم، ولم تحلَّ لأحد قبلي، وأُعْطِيتُ الشفاعة، وكان النبي يُبْعَثُ إلى قومه خاصة، وبُعِثتُ إلى الناس عامَة».
[صحيح] - [متفق عليه]
المزيــد ...

Daga Jabir Dan Abdullah -Allah ya yarda da su- zuwa ga Annabi: "An bani abubuwa biyar, wadanda ba a baiwa wani daga cikin Annabawa a gabani na ba : An bani cin nasara ta hanyar tsoro (da ake jefawa abokan gaba) wata daya gabanin haduwar mu, kuma aka sanya mini kasa ta zama wajen yin sallah na kuma abar yin tsarki,don haka duk wanda salla ta riske shi cikin al'umma ta to sai ya yi ta, kuma an halarta min ganima, ba'a taba halartawa wani kafin ni ba, kuma an bani ceto, ya kasance ana aiko Annabi zuwa ga mutanensa kadai , Ni kuwa an aiko ni zuwa ga mutane gaba daya
Ingantacce ne - Bukhari da Muslim suka Rawaito shi

Bayani

An kebance Annabinmu da wasu dabi'u madaukaka, kuma aka banbanta shi da wasu kyawawan abubuwa akan sauran Annabawa Allah ya yi aminci gare su,sai Al'ummar Annabi suka sami falaloli masu gairma da albarkar wannan Annabin mai albarka,daga cikinsu:Ya tabbata a wannan hadisin na wadannan abubuwa biyar massu girma: Na farko:Allah Madaukaki ya tamaki Annabi da jefa tsoro cikin zukatan abokan gaba, wanda ke raunana su ya tarwatsa su tun suna nisan tafiyar wata daya da shi, don karfafar Annabi da nasara akan abokac gabarsa da kuma karya makiya addininsa, lallai wannan taimako ne mai girma daga Allah Madukaki.Na biyu:Allah Madaukaki ya yalwata wa Annabi Mai girma, da al'ummasa ta hanyar mayar musu da kasa ta zama msallaci, duk inda salla ta riske su sai su yi ta, ba'a yi musu iyaka da wani guri kebantacce ba, kamar yadda aka aka yiwa wanda suka gabace su. don basu yin ibada sai acikin coci-coci ko a wuraren bauta, sai Allah ya cire kunci ga wannan al'ummar, saboda falala da kyautatawa,da baiwa,hakanan wanda suka gabaci wannan al'ummar ba su yin tsarki,dole sai da ruwa, wannan al'ummar kuma aka sanya ga wanda bai sami ruwa ba, kasa ta zame masa abin yin tsarki, hakanan wanda ya gaza amfani da ruwa don wata larura.Hakanan an halartawa Annabi da al'ummarsa ganimar da aka karba a hannun kafirai ko mayaka, sai su raba ta tsakaninsu da Allah Madaukaki, bayan ta kasance an haramta ta ga Annabawan da suka gabaci Aannabi su da al'ummarsu, sun kasance suna tara ganima, idan Allah ya karba sai ya saukar da wuta daga sama ta kone ta.Na hudu Allah Madaukaki, ya kebance Matsayi Abin godewa, da Ceto Mafi girma ga Annabi a ranar da za'a jinkirta Mafiya girman daraja daga Manzanni, sai Annabi ya gabata yace: Ni nake da ita, sai ya yi sujjada karkashin Al'arshi, ya gimama Allah Madaukaki da abin da ya dace da shi, sai a ce:nemi ceta abaka damar yin ceton, ka roka a baka, to a nan ne Annabi zai nemiwa al'umma ceto da falala a tsakaninsu a wannan bagiren mai tsawo, wannan shi ne, Bagire Abin dodewa wanda Al'ummar farko da ta karshe ke yiwa Annabi gibda a kanasa na Na biyar: d Dukkanin Annabawa da suka gabata an kebance kiransu zuwa ga al'ummarsu kawai.Amma Allah Madaukaki ya sanya wannan shariar ta dace da kowane lokaci da kuma ko wane waje, tun da ta kasance ta dace saboda dacewarta ne ma yasa ta zama itace ta karshe, don bata bukatar dadi ko ragi,an sanya ta ta game koma don ginshikan da ke cikinta masu sanya dawwama da wanzuwa.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Swahili
Manufofin Fassarorin