عن يحيى المازني رحمه الله قال: ((شَهِدتُّ عمرو بن أبي حسن سأل عبد الله بن زيد عن وُضوء النبي صلى الله عليه وسلم ؟ فدعا بتَور من ماء، فتوضَّأ لهم وُضُوء رسول الله صلى الله عليه وسلم ، فأكفَأ على يديه من التَّورِ، فغسَل يديه ثلاثًا، ثم أدخل يدهُ في التور، فمَضْمَض واسْتَنْشَق واسْتَنْثَر ثلاثا بثلاثِ غَرَفَات، ثم أدخل يده فغسل وجهه ثلاثا، ثم أدخل يده في التور، فغَسَلَهُما مرَّتين إلى المِرْفَقَين، ثم أدخل يدَه في التَّور، فمَسَح رأسَه، فأَقْبَل بهما وأَدْبَر مرَّة واحدة، ثم غَسَل رِجلَيه)). وفي رواية: ((بدأ بمُقَدَّم رأسه، حتى ذَهَب بهما إلى قَفَاه، ثم رَدَّهُما حتَّى رَجَع إلى المكان الذي بدأ منه)). وفي رواية ((أتانا رسول الله صلى الله عليه وسلم فأخْرَجنا له ماء في تَورٍ من صُفْرٍ)).
[صحيح] - [الرواية الأولى: متفق عليها الرواية الثانية: متفق عليها الرواية الثالثة : رواها البخاري]
المزيــد ...

Daga Yahya Almaziny Allah masa rahama yace: [Na ga Amru Dan Abul Hasan ya tambayi Abdullahi Dan Zaidu game da alwallar Annabi -tsira da aminci su tabbata a gare shi- sai yasa a kawo masa abin alwalla, sai yayi musu alwalla irin alwallar Manzon Allah -tsira da aminci su tabbata a gare shi- sai ya karkata abin alwallar ya zuba ruwa a hannayansa, sai ya wanke hannayensa sau uku, sannan ya shigar da hannnunsa cikin abin alwallar, ya kurkure bakinsa ya shaka ruwa a hanci ya face sau uku da kamfata uku, sannan ya kuma shigar da hannunsa ya wanke fuskarsa sau uku, sannan ya kuma debo ruwa daga abin alwallar ya wanke hannayensa zuwa gwuiwoyin hannunsa sau biyu sannan ya kuma sa hannunsa cikin abin alwalla, sai ya shafi kansa, ya yo gaba ya yi baya dasu sau daya, sannan ya wanke kafafuwansa]. A wata ruwayar: [Ya fara daga goshinsa, har zuwa keyarsa sannan ya dawo dasu inda ya fara]. A wata ruwayar: [Manzo tsira da amincin Allah ya zo mana sai muka kawo masa ruwa a cikin mazubin da aka yi shi da sufr]
Ingantacce ne - Buhari ne ya rawaito shi

Bayani

Yana daga kwadayin magabata na gari akan bin sunna -Allah yayi musu rahama-, sun kasance suna tambayar yadda Annabi ke yin ayyuka tsira da aminci su tabbata a gare shi; don suyi koyi da shi acikin ayyukan, a wannan hadisin Amr Dan Yahya Almaziny daga babanshi yana bamu labarin cewa: shi ya ga Baffansa Amru Dan Abi Hasan, yana tambayar Abdullahi Dan Zaidu daya daga sahabbai Allah ya yarda dashi game da alwalar Annabi tsira da aminci su tabbata a gare shi: Sai Abdullahi ya so yayi bayanin alwallar a aikace; don kuwa anfi saurin ganewa, kuma yafi tabbata cikin zuciya, sai yasa aka kawo masa abin alwalla, sai ya fara da wanke tafukansa da farko; saboda sune ake yin alwallar dasu dasu kuma ake debo ruwan, sai ya tuntsuro abin alwallar ya wanke su sau uku,sannan ya shigar dasu cikin abin alwallar, sannan ya kamfata sau uku ya wanke fuskarsa, ya kuma kamfata ya wanke hannayensa zuwa gwuiwar hannu sau biyu, ya kuma shigar da hannunsa cikin abin alwallar ya shafi kansa da hannayensa ya fara daga goshinsa har zuwa keyarsa, sannan ya dawo dasu har zuwa inda ya fara, ya yi haka ne don ya shafi gashin gaba da baya don kuma ya shafi ko ina da ina, sannan ya wanke kafafunsa zuwa idon sawu, Abdullahi Dan Zaidu -Allah ya yarda dashi ya bayyana mana cewa haka Manzo tsira da aminci yayi lokacin da yazo musu, aka fito masa da abin alwalla wanda aka yi shi daga sufr; Don yayi alwalla, Abdullahi ya bayyana haka ne don ya tabbatar da cewa shi yana da tabbas cikin lamarin.

Fassara: Turanci Fassara Yaren Faransanci Sifaniyanci Turkiyanci urdu Indonisiyanci Bosniyanci Rashanci Fassarar Bangaliyanci Fassara da Yaren Chanise Farisanci Tagalog Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Vietnam Sinhalese Uighur Kurdawa Portuguese Malayalam Swahili bushtu Asami السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية الدرية
Manufofin Fassarorin