عن عبد الله بن مَسعود رضي الله عنه قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صلى الله عليه وسلم : «أَوَّلُ مَا يُقْضَى بَيْنَ النَّاسِ يَوْمَ الْقِيَامَةِ فِي الدِّمَاءِ».
[صحيح] - [متفق عليه، واللفظ لمسلم]
المزيــد ...
Daga Abdullahi Dan Mas'ud Allah ya yarda da shi- zuwa ga Annabi: "Farkon abin da zaa fara yin hukunci akansa ran kiyama shi ne jinane."
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim Suka Rawaito shi amma lafazin na Muslim ne]
Allah zai yiwa halittunsa hisabi ranar kiyam, sannan sai yayi hukunci a tsakaninsu da adalcinsa, zai fara da abin da ya shafi zalunci, kasancewar jinane sune mafi girman abu cikin zalunci sune farkon abin da za'a fara dasu a wannan ranar, wannan a tsakanin bayi kenan, amma game da ayyukan bayi kuwa salla itace farkon abin da za'a kalla.