+ -

عَنْ عَبْدِ اللهِ بنِ مَسْعُودٍ رضي الله عنه قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«أَوَّلُ مَا يُقْضَى بَيْنَ النَّاسِ يَوْمَ الْقِيَامَةِ فِي الدِّمَاءِ».

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح مسلم: 1678]
المزيــد ...

Daga Abdullahi Dan Mas’ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"Farkon abinda za’a yi huknci a tsakanin mutane a ranar Alkiyama akan jini ne".

Ingantacce ne - Bukhari da Muslim Suka Rawaito shi amma lafazin na Muslim ne

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ambaci cewa farkon abinda za’a yi hukunci a tsakanin mutane a zalincin junansu a ranar Alkiyama: A jinane ne, kamar kisa da raunuka.

Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Malayalam Telgonci Swahili Yaran Tailand bushtu Asami السويدية الأمهرية الغوجاراتية القيرقيزية النيبالية اليوروبا الدرية الصومالية الكينياروندا الرومانية التشيكية المالاجاشية
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Girman al'amarin jinane, domin farawa tana kasancewa ne da abu mafi muhimmanci.
  2. Zunubai suna girmama ne da gwargwadan barnar da take afkuwa da su, salwantar da rayuka kubutattu yana daga mafi girman barna babu mafi girma daga gare shi sai kafirci da yi wa Allah - Madaukakin sarki - shirka.