+ -

عَنْ أَبِي مُوسَى الأَشْعَرِيِّ رضي الله عنه قَالَ:
أَتَيْتُ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ فِي رَهْطٍ مِنَ الأَشْعَرِيِّينَ أَسْتَحْمِلُهُ، فَقَالَ: «وَاللَّهِ لاَ أَحْمِلُكُمْ، مَا عِنْدِي مَا أَحْمِلُكُمْ» ثُمَّ لَبِثْنَا مَا شَاءَ اللَّهُ فَأُتِيَ بِإِبِلٍ، فَأَمَرَ لَنَا بِثَلاَثَةِ ذَوْدٍ، فَلَمَّا انْطَلَقْنَا قَالَ بَعْضُنَا لِبَعْضٍ: لاَ يُبَارِكُ اللَّهُ لَنَا، أَتَيْنَا رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ نَسْتَحْمِلُهُ فَحَلَفَ أَنْ لاَ يَحْمِلَنَا فَحَمَلَنَا، فَقَالَ أَبُو مُوسَى: فَأَتَيْنَا النَّبِيَّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ فَذَكَرْنَا ذَلِكَ لَهُ، فَقَالَ: «مَا أَنَا حَمَلْتُكُمْ، بَلِ اللَّهُ حَمَلَكُمْ، إِنِّي وَاللَّهِ -إِنْ شَاءَ اللَّهُ- لا أَحْلِفُ عَلَى يَمِينٍ، فَأَرَى غَيْرَهَا خَيْرًا مِنْهَا، إِلَّا كَفَّرْتُ عَنْ يَمِينِي، وَأَتَيْتُ الَّذِي هُوَ خَيْرٌ».

[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 6718]
المزيــد ...

Daga Abu Musa al-Ash'ari - Allah Ya yarda da shi - ya ce:
Na zo wa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin wasu mutane daga Ash'arawa ina neman ya dauki nauyinmu, sai ya ce: "Wallahi ba zan dauki nauyinku ba, bani da abinda zan dauki nauyinku" Sannan muka zauna lokacin da Allah Ya so, sai aka zo da wasu rakuma, sai ya yi mana umarni da rakuma uku, lokacin da muka tafi sai sashinmu suka ce da sashi: Allah ba Zai yi mana albarka ba, mun zowa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - muna neman ya dauki nauyinmu sai ya yi rantsuwa cewa ba zai dauki nauyinmu ba sai kuma ya dauki nauyinmu, sai Abu Musa ya ce: sai muka zo wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai muka ambata masa hakan, sai ya ce: "Ba nine na ɗauki nauyinku ba, a’a Allah ne Ya ɗauki nauyinku, Lallai ni wallahi - in Allah Ya so - bana rantsuwa, sai inga waninta mafi alheri daga gareta. sai na yi kaffarar rantsuwata, kuma nazowa wanda shi ne mafi alherin".

[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [صحيح البخاري - 6718]

Bayani

Abu Musa Al’Ash'ari - Allah Ya yarda da shi - yana bada labarin cewa shi ya zo wurin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a tare da shi akwai wasu jama'a daga kabilarsa, manufarsu ita ce Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya basu rakuman da zasu hau; dan samun damar fita yaki, sai tsira da aminci su tabbata agare shi ya yi rantsuwar cewa ba zai dauki nauyin su ba, ba shi da abinda zai dauki nauyinsu da shi, sai suka koma suka zauna tsawon wani lokaci, sannan wasu rakuma uku suka zo wa tsira da amincin Allah su tabbata agare shi, sai ya aika musu, sai sashinsu ya cewa sashi: Allah ba zai yi mana albarka a wadannan rakuma ukun ba; domin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi rantsuwar cewa ba zai dauki nauyinmu ba, sai suka zo masa suka tambaye shi , sai tsira da aminci su tabbata agare shi ya ce: Wanda ya dauki nauyinku Shi ne Allah - Madaukkain sarki -; domin cewa Shi ne Mai datarwa kuma Mai azirtawa, kadai ni sababi ne wanda hakan ya gudana ta hannuna, sannan tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: Lallai ni na rantse da Allah, idan Allah Ya so ba na rantsuwa akan wani abu da aikata shi ko na bar shi, kuma in ga wanin wannan abinda na rantse akansa shi ne mafi alheri, sai na aikata abinda yafin kuma in bar wanda na rantse akansa din, kuma in yi kaffarar rantsuwa ta.

Fassara: Turanci urdu Sifaniyanci Indonisiyanci Uighur Fassarar Bangaliyanci Fassara Yaren Faransanci Turkiyanci Rashanci Bosniyanci Sinhalese Kwafar laakwalwar zuwa bugere fassara Fassara da Yaren Chanise Farisanci Vietnam Tagalog Kurdawa Portuguese Malayalam Swahili Yaran Tailand bushtu Asami السويدية الأمهرية الهولندية الغوجاراتية Kirgisisch النيبالية الدرية الرومانية Oromo
Manufofin Fassarorin

Daga Cikin Fa idodin Hadisin

  1. Halaccin rantsuwa ba tare da ansa a yi rantsuwa ba; dan karfafa labari koda ya kasance a nan gaba ne.
  2. Halaccin togaciya da fadinsa: In Allah Ya so", bayan rantsuwa, kuma togaciya idan an yi niyya tare da rantsuwa, kuma hakan ya kasance a hade da rantsuwar to kaffara bata wajaba akan wanda ya yi karya rantsuwarsa.
  3. Kwadaitarwa a kan sabawa rantsuwa idan ya ga waninta shi ne mafi alheri daga rantsuwar, kuma ya yi kaffarar rantsuwarsa.