عَنْ أَبِي هُرَيْرَةَ عَبْدِ الرَّحْمَنِ بْنِ صَخْرٍ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ قَالَ: سَمِعْت رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّم يَقُولُ:
«مَا نَهَيْتُكُمْ عَنْهُ فَاجْتَنِبُوهُ، وَمَا أَمَرْتُكُمْ بِهِ فَافْعَلُوا مِنْهُ مَا اسْتَطَعْتُمْ، فَإِنَّمَا أَهْلَكَ الَّذِينَ مِنْ قَبْلِكُمْ كَثْرَةُ مَسَائِلِهِمْ، وَاخْتِلَافُهُمْ عَلَى أَنْبِيَائِهِمْ».
[صحيح] - [رواه البخاري ومسلم] - [الأربعون النووية: 9]
المزيــد ...
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa:
«Duk abin da na haneku daga gare shi to ku nisance shi, kuma abinda na umarce ku da shi to ku zo da shi dai dai iyawarku, domin abin da ya halaka magabatanku (shi ne) yawan tambayoyinsu da kuma saɓawarsu ga Annabawansu».
-
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana mana cewa shi idan ya hana mu wani abu to ya wajaba a kanmu mu nisance shi, ba tare da togaciya ba, idan kuma ya umarce mu da wani abu to wajibi ne a kanmu mu aikata abin da zamu iya daga gare shi. Sannan ya gargaɗemu dan kar mu zama kamar wasu daga cikin al'ummun da suka gabata lokacin da suka yawaita tambayoyi ga Annabawan su tare da saɓa wa annbawan, sai Allah Ya yi musu uƙuba da nau'ikan halaka da rusawa, to yana kamata kada mu zama irinsu dan kada mu halaka kamar yadda suka halaka.