عَنِ ابْنِ عَبَّاسٍ رضي الله عنهما قَالَ: قَالَ رَسُولُ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ:
«إِنَّ اللَّهَ يُحِبُّ أَنْ تُؤْتَى رُخَصُهُ، كَمَا يُحِبُّ أَنْ تُؤْتَى عَزَائِمُهُ».  
                        
[صحيح] - [رواه ابن حبان] - [صحيح ابن حبان: 354]
                        
 المزيــد ... 
                    
Daga Dan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"Lallai Allah Yana son azo wa rangwaminSa, kamar yadda  yake son  azo wa yin aiki a asalinsa". 
                                                     
                                                                                                    
[Ingantacce ne] - [Ibnu Hibban ne ya Rawaito shi] - [صحيح ابن حبان - 354]                                            
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bada labarin cewa Allah Yana son azo wa rangwaminSa wadanda ya shara'antasu, na sauki a cikin hukunce-hukunce da ibadu, da saukakawa a cikinsu ga wanda aka dorawa shari'a - kamar kasarun sallah da kuma hada su a halin tafiya -. Kamar yadda cewa Shi Yana son azo wa azimarSa, daga al'amura wajibai; domin umarnin Allah a rangwame da wajibai daya ne.