عَنْ عَائِشَةَ أُمِّ المُؤْمِنينَ رَضِيَ اللَّهُ عَنْهَا قَالَتْ:
مَا صَلَّى النَّبِيُّ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ صَلاَةً بَعْدَ أَنْ نَزَلَتْ عَلَيْهِ: {إِذَا جَاءَ نَصْرُ اللَّهِ وَالفَتْحُ} [النصر: 1] إِلَّا يَقُولُ فِيهَا: «سُبْحَانَكَ رَبَّنَا وَبِحَمْدِكَ اللَّهُمَّ اغْفِرْ لِي».
وعَنْها قَالَتْ: كَانَ رَسُولُ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يُكْثِرُ أَنْ يَقُولَ فِي رُكُوعِهِ وَسُجُودِهِ: «سُبْحَانَكَ اللهُمَّ رَبَّنَا وَبِحَمْدِكَ، اللهُمَّ اغْفِرْ لِي» يَتَأَوَّلُ الْقُرْآنَ.
[صحيح] - [متفق عليه] - [صحيح البخاري: 4967]
المزيــد ...
Daga Nana Aisha Uwar Muminai - Allah ya yarda da ita - ta ce:
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai taɓayin wata sallah ba bayan saukar:
{Idan nasarar Allah ta zo da buɗi} [al-Nasr: 1] ta sauka gare shi sai ya ce a cikinta (sallar):
"Tsarki ya tabbatar maKa Ubangijinmu da godiyarKa ya Allah Ka gafarta mini'. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana yawan faɗa a cikin ruku'unsa da sujjadarsa: "Tsarki ya tabbatar maKa ya Allah Ubangijinmu da godiyarKa, ya Allah Ka gafarta mini" yana fassara alƙur'ani.
[Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi] - [Sahih Al-Bukhari - 4967]
Uwar muminai Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - tana bada labarin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - lokacin da aka saukar masa da: {Idan nasarar Allah ta zo da buɗi} ya fassara Alƙur'ani kuma ya yi gaggawa zuwa ruko da umarnin Allah - Maɗaukakin sarki - a cikin faɗinSa: {Ka yi tasbihi da godiyar Ubangijinka kuma ka nemi gafararSa}, to ya kasance yana yawaita faɗa a cikin halin ruku'insa da sujjadarsa a tsakiyar sallah: "Tsarki ya tabbatar maKa" da tsarkakewa gareKa daga dukkan tawaya daga abinda ba ya dacewa da Kai, "Ya Allah Ubangijinmu da godiyarKa" da yabo abin yabo gareKa dan cikar zatinka da siffofinKa da ayyukanKa, "Ya Allah Ka gafarta mini' Ka shafe mini zunubina Ka ƙetare daga gare shi .